Labarai
Tabbatar kana ganin likita akai-akai Don Hana Makanta – Dr. Avar

Dokta Gideon Avar, likitan ido, ya jaddada mahimmancin duba lafiyar mutanen da suka kai shekaru arba’in zuwa sama don hana makanta.
Kamar yadda Daraktan Likitoci na Cibiyar Ido ta Nobis da ke Jalingo, Jihar Taraba, Dokta Avar ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a asibitin ido na Nobis VIP da ke mil 6.
Duk da kalubalen da asibitinsa ke fuskanta, Dokta Avar ya ambata cewa suna sadaukarwa don taimaka wa majiyyata ta hanyar rage farashin kuɗin magani.
Ya bayyana cewa galibin ayyukan da suke yi na aikin agaji ne, kuma a wani bangare na ayyukansu na zamantakewar al’umma, sun samar da rijiyoyin burtsatse guda hudu a cikin al’ummar da suke zaune domin samar da ruwan sha kyauta ga mutane.
Dokta Avar ya bukaci daidaikun mutane, musamman wadanda suka haura shekaru arba’in da su ba da fifiko wajen duba lafiyar jama’a, domin rigakafin ya fi magani.
Ya kuma bayyana cewa ciwon ido da yana ne kan gaba wajen kawo makanta a Najeriya, inda ya ce asibitin na gudanar da aikin tiyatar ido ga mutane kusan dubu 3 a duk shekara.
Sani Sulaiman/Wababe
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
