Connect with us

Fasaha

Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Bai Wa Ɗalibai Rancen Kuɗin Karatu

Published

on

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kan dokar bai wa ɗalibai bashin karatu.

Ya sa hannu kan dokar ce a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a wannan Larabar.

Hakan na ƙunshe cikin wani saƙo da hadiminsa kan zaurukan sada zumunta, Dada Olusegun ya wallafa.

Dokar mai taken kudurin sauya wa dokar bai wa dalibai rancen karatu fasali ta 2024, an samar da ita ne domin kafa asusun tallafa wa ɗaliban makarantun gaba da sakandire.

A watan Nuwambar shekarar da ta wuce ne majalisar dokokin kasar ta amince da kudurin dokar, da ke neman kafa wata gidanauniyar da za ta riƙa ba daliban manyan makarantun kasar bashin kudin makaranta.

Sai dai ƙudirin ya fuskanci tasgaro dangane da wasu mas’aloli da suka shafi tsare-tsaren karɓa da biyan bashin kuɗin, lamarin da ya sanya Tinubu ya sake bitar ƙudirin tare da aike wa majalisa sabuwar buƙatar neman amincewarta.

A ranar 20 ga Maris, Majalisar Dattawa ta zartar da ƙudirin bayan nazarin rahoton kwamitinta da ke da alhakin kula da manyan makarantun da Asusun TETFUND da suka yi la’akari da kudirin.

Karkashin dokar bai wa ɗalibai rancen kuɗin karatu, za a ba da lamuni marar ruwa ga ’yan Najeriya da suka cancanci samun ilimi mai zurfi.

Masu ruwa da tsaki dai sun tabo batutuwan da suka shafi tsarin bayar da rancen kuɗin ga ɗalibai, musamman ma kan abin da ya shafi buƙatun cancanta, hanyoyin samar da kuɗaɗen, hanyoyin miƙa ɗalibai rancen da suka nema da kuma biyan bashin kuɗaɗen da sauran su.

Sabuwar dokar dai ita ce irinta ta farko a Najeriya a cewar Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila.

Gbajabiamila wanda shi ne ya kawo kudurin dokar lokacin yana kakakin majalisa, ya ce dokar za ta inganta kasar domin babu wani yaron Najeriya da za a hana wa damar samun ilmi mai zurfi saboda rashin kuɗi.

Bello Wakili/Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai21 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai23 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai23 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi1 day ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara