Connect with us

Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kwace Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 82 A Bauchi

Published

on

Daga Alhassan Usman 

Sashen Ayyuka na Tarayya, da ke Yanki na 4 a Bauchi, na Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS) wato Zone D, ya kwace kayayyakin fasa-kwauri da darajar harajinsu ta kai sama da Naira Miliyan 82 cikin makonni biyu.

Kwamandan Yankin, Abdullahi Kaila, ya bayyana hakan yayin taron manema labarai a Bauchi, inda ya ce jami’an sashen yaki da fasa-kwauri sun yi nasarar kwace kayayyakin tsakanin ranakun  8 zuwa 19 ga watan Disamban 2025.

Ya bayyana cewa Sashen na Ayyukan Tarayya ne ke da alhakin aiwatar da dokokin Kwastam, bin manufofin haraji na gwamnati da kuma dakile fasa-kwauri a jihohi tara, wadanda suka hada da Adamawa, Taraba, Bauchi, Gombe, Borno, Yobe, Plateau, Benue da Nasarawa.

Kaila ya kara da cewa an kara karfafa ayyukan yaki da fasa-kwauri a yankin, ta hanyar inganta hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu sa ido, yana mai jaddada cewa irin wannan hadin gwiwar na kara musayar bayanan sirri da aiwatar da ayyukan hadin kai wajen yakar kungiyoyin fasa-kwauri.

Ya bukaci ‘yan kasuwa a yankin da su kasance masu bin doka, su kuma guji haramtaccen kasuwanci, yana mai gargadin cewa ba za a bar wata mafaka ga masu aikata fasa-kwauri ba.

Kwamandan ya kuma ce sashen zai ba da muhimmanci ga wayar da kan jama’a, ta hanyar amfani da kafafen yada labarai da kuma kai ziyara yankuna daban daban, domin fadakar da jama’a game da illar fasa-kwauri ga tattalin arziki da kuma karfafa su su rika kai rahoton haramtattun ayyuka.

Labarai

Labarai23 hours ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai23 hours ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai23 hours ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai23 hours ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai23 hours ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai2 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai2 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai3 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai4 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara