Labarai
Hukumar Kwastam ta Kasa Ta Samu Sabon Shugaba a Jihar Kwara
Daga Ali Muhammad Rabi’u
Tsohon Kwamandan Hukumar Hana Fasakwauri ta Kasa, shiyyar jihar Kwara, Comptroller Faith Ojeifo, ya yi kira ga jami’ai da ma’aikata da su bai wa sabon mukaddashin kwamanda da aka tura cikakken goyon baya domin ya samu nasara a aikinsa.
Comptroller Ojeifo ya bayyana hakan ne yayin bikin mika mulki a hukumance ga sabon Mukaddashin Kwamandan Yanki, DC Najeem Ogundeyi, a birnin Ilori.
Ya nuna godiyarsa ga dukkan jami’ai da ma’aikatan hukumar, hukumomin tsaro na ‘yan uwa, da sauran masu ruwa da tsaki, bisa gagarumin hadin kai da suka nuna masa a lokacin mulkinsa.

“Mun samu nasarori masu yabawa tare, musamman a fannonin tara kudaden shiga, aiwatar da dokoki, da inganta ayyukan hidima,” in ji shi.
Comptroller Ojeifo ya bayyana cikakken kwarin gwiwarsa kan kwarewar shugabanci, gogewa da kuma kwararrun halayen Mukaddashin Kwamandan, DC Najeem Akanmu Ogundeyi.
Ya bukaci dukkan jami’ai da ma’aikata da su ba shi cikakken goyon baya, biyayya da hadin kai domin tabbatar da nasararsa.

A nasa bangaren, Mukaddashin Kwamandan Yanki, DC Najeem Akanmu Ogundeyi, ya nuna godiyarsa ga Babban Kwamandan Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi MFR, FNIPR, PhD, da kuma tawagarsa ta gudanarwa bisa wannan dama ta musamman da aka ba shi domin yi wa kasa hidima a wannan matsayi.
Ya kuma nuna matukar godiya da yabo ga Comptroller Faith Mathew Ojeifo mai ritaya bisa jajircewarsa, kwarewarsa da kyakkyawan shugabanci a tsawon lokacin mulkinsa. Ya ce jajircewarsa wajen aiki, ladabi da hidima sun kafa tubali mai karfi da wannan runduna za ta ci gaba da ginawa a kai.
Mukaddashin Kwamandan ya kara da cewa tsarin shugabancinsa zai ta’allaka ne kan girmama juna, bin doka da oda sosai, da kuma jajircewa wajen inganta ayyukan hukumar. Za a karfafa gwiwar kowane jami’i da ma’aikaci ya bayar da iyakar kokarinsa, domin nasarar mu ta bai daya tana rataye ne a kan hadin kanmu gaba daya.
Sabon kwamandan ya yi kira ga dukkan jami’ai da su nuna masa irin hadin kai, goyon baya da jajircewar da suka bai wa magabacinsa.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
