Connect with us

Labarai

Kungiyar ‘Yan Sintiri Ta Bayyana Rashin Goyon Bayanta Kan Kafa ‘Yan Sandan Jihohi

Published

on

Babban kwamandan Kungiyar ‘Yan sintiri ta Sakai ta kasa da aka fi sani da “Vigilante Group of Nigeria,” ya bayyana rashin goyon bayansu na kafa ‘Yansandan jihohi a Najeriya.

Babban kwamandan kungiyar Nebi Kaftin mai ritaya, Umar Bakori ya ce ba sa goyon bayan kafa Yansandan Jihohi a Najeriya, bayan da Kungiyar ta gabatar da gyare-gyare da ta ke so a yi a Kundin Tsarin Mulki ga kwamatin tsaro na Majalisar Wakilai a ranar Talatan nan.

Kaftin Bakori ya ce wannan yunkuri na kafa Yansandan Jihohi wata hanyace da ake amfani da ita wajen cinhanci da rashawa ta hanyar kwasar makudan kudade da sunan samar da tsaro.

Bakori ya ce Gwamnatin Taraiya ta kashe sama da Naira biliyan 13 don samar da Yansandan Al’umma amma hakan ya wuce babu wani canji da aka samu.

Ya bayar da misali da ikirarin Gwanonin Jihohin Katsina da Zamfara suka yi na cewa jihar Zamfarar ta kashe naira biliyan 10 kana jihar katsina ta kashe naira bilyan 17 domin samar da tsaro a jihohin su, sai dai acewarsa hakan bai samar da tsaron da a ke bukata ba a jihihin kawo yanzu

Ya ce Gwamnatin Jihar Ekiti ta kashe naira biliyan 1.4 da Jihar Ondo sun kashe naira biliyan 2 amma ba wata nasara.

In da ya ce a maimKon ha ka kamata ya yi gwamnonin su su tallafawa Kungiyar Vigilante don samar da tsaro a jihohin na su.

Kazalika ya kara da cewa tuni Kungiyar ta Vigilante na da mambobi sama da miliyan daya a Najeriya.

Kaftin Bakori ya ce mambobin su na da masaniya na wuraren da suke aiki kuma yan asalin yankin ne, sabo da haka suna da masaniya na lungu da sako na inda ma su laifi su ke, Sabo da haka suna taimakawa jami’an tsaro da bayanan sirri yadda ya da ce.

Ya ce Kungiyar ta su tana bukatar gwamnati ta amince da su kana ta basu kulawar da ta kamata ta hanyar basu tallafi na kudade a zama wani mataki na karfafa mu su gwiwa na cigaba da yin abun da suka sa kansu sama da shekaru 30 da suka gabata.

Shugaban ya bukaci Gwamnati ta samar da wata cibiya da za ta rinka bawa Yan Vigilante horo da Tsare-tsare da Dokoki don kyautata aikin su ta re da samar musu da kayan aiki da zai taimaka wajen samun nasarar aikin da su ke yi na rabbatar da tsaro a kasa.

Kwamandan ya nuna jin dadi na yadda Sojoji su ke basu hadin kai da goyon bayan ta yin aiki tare da juna, wanda hakan ya haifar da nasarori wajen kubutar da ‘Yan makarantar da aka yi garkuwa da su a Kuriga da Chibock da sauran wurare makamanta.

 

COV/Bashir M

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Kasuwanci15 hours ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha18 hours ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha18 hours ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai18 hours ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai4 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai6 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai6 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai6 days ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai1 week ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Mafi Shahara