Connect with us

Ilimi

Zaben Shugaban BUK: Farfesa Haruna Musa Ya Yi Wa Sauran ‘Yan Takara Zarra

Published

on

Mataimakin Shugaban Jami’ar Bayero Kano a harkokin karatu, kuma ƙwararre a fannin Kimiyyar Roba, Farfesa Haruna Musa, ya bayyana a matsayin ɗan takarar da ya fi samun karɓuwa a zaɓen sabon Shugaban Jami’ar Bayero Kano (BUK) da ake gudanarwa.

 

Sakamakon ya biyo bayan taron hadin gwiwar na bakwai (7th Congregation Parley) da aka gudanar a ranar Talata, 1 ga Yuli, 2025, inda Farfesa Musa ya samu ƙuri’u 853, ya bar sauran ‘yan takara hudu a baya da tazara mai yawa.

 

Tsarin zaɓen ya gudana  bisa nagarta da kulawa, wanda ya nuna goyon baya mai ƙarfi daga malamai da manyan ma’aikatan gudanarwa na BUK.

Farfesa Mahmoud Umar Sani tsohon Mataimakin shugaban jami’ar kan Harkokin Gudanarwa ya sami ƙuri’u 367, yayin da Farfesa Sani Muhammad Gumel (tsohon mataimakin  shugaban jami’ar kan harkokin karatu ya sami ƙuri’u 364, sai Farfesa Adamu Idris Tanko, tsohon mataimakin shugaban jami’a kan harkokin karatu da gudanarwa ya sami ƙuri’u 161, shi kuma Farfesa Bashir FaFaggya sami ƙuri’u 18.

 

Jimillar masu kada ƙuri’a da aka tantance su ita ce 1,784, inda shugaban kwamitin zaɓe, Farfesa Muhtari Ali Hajara, ya bayyana cewa ƙuri’u 17 ba su da inganci yayin da guda huɗu ba a bayyana su ba.

 

Da yake jagorantar taron, Shugaban jami’ar mai barin gado, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya jaddada cewa ko da yake ƙuri’ar amincewar jama’a tana da kaso 20 bisa dari, cikin tsarin zaɓen gaba ɗaya, tana taka muhimmiyar rawa wajen shawarwarin da kwamitin gudanarwar jami’ar zai yanke.

 

Wannan tsari yana nuna ƙarfin tsarin dimokuradiyya da gaskiya da jami’ar mu ta tanada.” In ji shi

A wani mataki na nuna ɗabi’ar kishin jami’a, ɗaya daga cikin fitattun ‘yan takarar, Farfesa Sani Muhammad Gumel, ya amince da sakamakon zaɓen, inda ya bayyana shi da cewa “an gudanar da shi bisa gaskiya da adalci ” tare da alkawarin ba da cikakken goyon baya ga Farfesa Haruna Musa.

 

Tsohuwar Ministar Ilimi, Farfesa Rukayyatu Ahmed Rufa’i, da tsohon Shugaban Jami’ar NOUN, Farfesa Abdalla Uba Adamu, sun taya shugabannin BUK murna bisa kyakkyawan tsari da kuma cigaban jami’ar.

 

Yanzu dai, hukuncin ƙarshe na wanda zai zama sabon Shugaban Jami’ar BUK na hannun Kwamitin Gudanarwar Jami’ar, wanda zai yi la’akari da kwarewa, hangen nesa, ƙwarewar gudanarwa da kuma amincewar jama’a kafin yanke shawara.

 

Tsarin zaɓen ya samu yabo daga fitattun mutane a fannin ilimi.

 

Daga Khadijah Aliyu

 

 

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara