Ilimi
Zaben Shugaban BUK: Farfesa Haruna Musa Ya Yi Wa Sauran ‘Yan Takara Zarra
Mataimakin Shugaban Jami’ar Bayero Kano a harkokin karatu, kuma ƙwararre a fannin Kimiyyar Roba, Farfesa Haruna Musa, ya bayyana a matsayin ɗan takarar da ya fi samun karɓuwa a zaɓen sabon Shugaban Jami’ar Bayero Kano (BUK) da ake gudanarwa.
Sakamakon ya biyo bayan taron hadin gwiwar na bakwai (7th Congregation Parley) da aka gudanar a ranar Talata, 1 ga Yuli, 2025, inda Farfesa Musa ya samu ƙuri’u 853, ya bar sauran ‘yan takara hudu a baya da tazara mai yawa.
Tsarin zaɓen ya gudana bisa nagarta da kulawa, wanda ya nuna goyon baya mai ƙarfi daga malamai da manyan ma’aikatan gudanarwa na BUK.

Farfesa Mahmoud Umar Sani tsohon Mataimakin shugaban jami’ar kan Harkokin Gudanarwa ya sami ƙuri’u 367, yayin da Farfesa Sani Muhammad Gumel (tsohon mataimakin shugaban jami’ar kan harkokin karatu ya sami ƙuri’u 364, sai Farfesa Adamu Idris Tanko, tsohon mataimakin shugaban jami’a kan harkokin karatu da gudanarwa ya sami ƙuri’u 161, shi kuma Farfesa Bashir FaFaggya sami ƙuri’u 18.
Jimillar masu kada ƙuri’a da aka tantance su ita ce 1,784, inda shugaban kwamitin zaɓe, Farfesa Muhtari Ali Hajara, ya bayyana cewa ƙuri’u 17 ba su da inganci yayin da guda huɗu ba a bayyana su ba.
Da yake jagorantar taron, Shugaban jami’ar mai barin gado, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya jaddada cewa ko da yake ƙuri’ar amincewar jama’a tana da kaso 20 bisa dari, cikin tsarin zaɓen gaba ɗaya, tana taka muhimmiyar rawa wajen shawarwarin da kwamitin gudanarwar jami’ar zai yanke.
“Wannan tsari yana nuna ƙarfin tsarin dimokuradiyya da gaskiya da jami’ar mu ta tanada.” In ji shi

A wani mataki na nuna ɗabi’ar kishin jami’a, ɗaya daga cikin fitattun ‘yan takarar, Farfesa Sani Muhammad Gumel, ya amince da sakamakon zaɓen, inda ya bayyana shi da cewa “an gudanar da shi bisa gaskiya da adalci ” tare da alkawarin ba da cikakken goyon baya ga Farfesa Haruna Musa.
Tsohuwar Ministar Ilimi, Farfesa Rukayyatu Ahmed Rufa’i, da tsohon Shugaban Jami’ar NOUN, Farfesa Abdalla Uba Adamu, sun taya shugabannin BUK murna bisa kyakkyawan tsari da kuma cigaban jami’ar.
Yanzu dai, hukuncin ƙarshe na wanda zai zama sabon Shugaban Jami’ar BUK na hannun Kwamitin Gudanarwar Jami’ar, wanda zai yi la’akari da kwarewa, hangen nesa, ƙwarewar gudanarwa da kuma amincewar jama’a kafin yanke shawara.
Tsarin zaɓen ya samu yabo daga fitattun mutane a fannin ilimi.
Daga Khadijah Aliyu
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
