Connect with us

Kasuwanci

Hukumar Kwastam Ta Mayar Da Tirela 6 Na Kayan Abinci Da Ta Kwace A Katsina

Published

on

Hukumar kwastam ta mayar da Tirela shidda na buhunan abinci da ta kama a Kongolam da ke kan iyakar Katsina da Jamhuriyar Nijar a a karamar hukumar Maiaduwa ta jihar Katsina.

Wannan dai ya yi dai-dai da umarnin shugaban kasa kamar yadda shugaban hukumar kwastam ta Nijeriya, Bashir Adeniyi ya sanar yayin wata ganawa da ya yi da al’ummar yankin iyakar Kongolam a karshen mako.

A lokacin da yake mika motocin guda shida dauke da hatsi a ofishin hukumar kwastam da ke Katsina, shugaban hukumar shiyar Jihar Katsina, Muhammad Umar, ya bayyana cewa an saki buhunan abincin ne ga masu su da sharadin cewa za a sayar da su a kasuwannin Najeriya kawai.

Ya ce jami’an hukumar kwastam sun kwace kayayyakin ne domin aiwatar da dokar hana fitar da kayayyakin abinci da shigo da su daga kasashen waje saboda karancin abinci da hauhawar farashin kayayyaki da ake fuskanta a kasar a halin yanzu.

Kwanturola Umar ya umarci masu wadannan kayayyakin su kasance masu kishin kasa tare da bin ka’idar siyar da kayan abinci a cikin Nijeriya a matsayin hanyar da za ta ci gaba da kokarin tabbatar da wadatar abinci.

Ya kuma kara da cewa, jami’an hukumar tare da hadin gwiwar jami’an Leken asiri da tawagar rundunar hadin gwiwa da ke sintiri a kan iyakokin kasar nan za su sa ido , domin tabbatar da cewa ba a fitar da wadannan kayayyakin daga kasar nan ta barauniyar hanya ba.

Kwanturolan na yankin Katsina ya kuma roki jama’a da su bayar da bayanan da za su taimaka wajen dakile safarar kayayyakin abinci da haramtattun kayayyaki daga kasar nan.

A jawabinsa yayin mika kayayyakin, shugaban kwamitin kula da samar da abinci na jihar Katsina, Jabiru Tsauri, ya gargadi masu safarar kayayyaki da masu motocin da aka sako da su bi umarnin shugaban kasa ta hanyar sayar da hatsin a kasuwannin Najeriya kawai.

Isma’il Adamu

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai11 hours ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai12 hours ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci1 day ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha2 days ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha2 days ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai2 days ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai7 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai7 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Mafi Shahara