Kasuwanci
Gwamnan Kabawa Ya Tabbatarwa Ma’aikatan Gwamnati Ingantacciyar Walwala
Gwamnatin jihar Kebbi, ta baiwa ma’aikatan jihar tabbacin ci gaba da jajircewa wajen kyautata jin dadin su da kuma kare hakkokinsu.
Gwamna Nasir Idris wanda ya ba da wannan tabbacin a lokacin da yake jawabi ga ma’aikata domin bikin ranar watan Mayu a Birnin Kebbi, ya jaddada cewa ma’aikata aminai ne masu kima wajen ci gaban jihar Kebbi, kuma su kasance masu ruwa da tsaki da ba za a yi watsi da su ba.
Gwamna Idris, wanda ya bayyana bikin ranar Mayu a matsayin wani muhimmin lokaci, ya yabawa ma’aikatan bisa jajircewarsu da irin gagarumar gudunmawar da suke bayarwa wajen ci gaban jihar.
“Kwazonku da jajircewarku sune kashin bayan tattalin arzikinmu. Ina yaba muku kan kokarinku na jajircewa”.
Gwamna Idris, ya kuma amince da kalubalen da ma’aikatan jihar ke fuskanta tare da ba su tabbacin gwamnatinsa ta kudiri aniyar magance wadannan matsalolin.
A yayin da yake taya kungiyar kwadago ta Najeriya NLC da TUC murnar zagayowar ranar ma’aikata, Gwamna Idris ya nuna jin dadinsa ga kungiyar ‘yan kasuwa bisa jajircewar da suke yi na kyautata jin dadin ma’aikata sannan ya bukaci ma’aikata da su ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukansu tare da ci gaba da ciyar da jihar gaba.
Tun da farko a nasa jawabin, shugaban kungiyar kwadago ta kasa (NLC) na jihar, Kwamared Murtala Usman, ya bayyana jin dadinsa a madadin kungiyoyin NLC da TUC bisa yadda Gwamnan ya ba da kulawar da yake yi wajen kyautata jin dadin ma’aikata da ci gaban su.
Kwamared Usman ya yaba da irin goyon bayan da Gwamnan ke ci gaba da baiwa ma’aikata, inda ya bayyana halartan taron bikin ranar Mayun 2025 kamar yadda aka zata duba da tarihinsa a matsayinsa na tsohon dan kungiyar kwadago da kuma tsohon shugaban kwadago.
Muhimman abubuwan da suka wakana a wajen taron sun hada da fareti da ma’aikata suka yi, da bayar da lambar yabo ga gwamna Idris da kungiyar dalibai ta kasa (NANS) reshen jihar Kebbi da kungiyar ma’aikatan jinya ta kasa suka yi.
Shugabannin kungiyar NLC na jihar sun kuma mika kyautuka ga wasu fitattun mutane bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban jihar Kebbi.
COV/ Abdullahi Tukur
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
