Connect with us

Ilimi

PCN Ta Kai Ziyara Ga Hukumar Samarda Magunguna Ta Jihar Kano

Published

on

Hukumar Kula da Magunguna ta Najeriya (PCN) ofishin Kano ta kai ziyarar gani da ido ga hukumar samar da magunguna ta jihar Kano (DMCSA).

 

Wannan ziyarar alama ce ta farkon tsarin ba da izini ga DMCSA don zama cibiyar rarraba magunguna ta mega da cibiyar bada horo.

 

Jami’ar Jihar Kano mai kula da ofishin PCN Kano Pharmacist Hasiya Abubakar Ladan ce ta jagoranci tawagar da suka kai ziyarar.

 

Wannan ziyarar wani mafari ne na tantancewa da wata tawagar kwararru daga hedikwatar PCN ta kasa da ke Abuja.

 

Ta bayyana cewa ziyarar na da nufin tantance yadda DMCSA ke bin ka’idoji, don ba da Takaddar Rijistar wuraren sayarda magunguna.

 

Pharmacist Ladan ta yabawa shugabannin DMCSA bisa yadda suke tafiyar da ayyukan kungiyar yadda ya kamata tare da nuna gamsuwa da matakin da hukumar ta dauka.

 

Darakta Janar na DMCSA Pharmacist Gali Sule, ya tarbi tawagar inda ya zagaya da su a rumbunan adana kayayyaki.

 

Ya bayyana cewa hukumar ta dakatar da samar da magunguna domin inganta sashin sarrafa magunguna kamar yadda PCN da NAFDAC suka bada shawara.

 

Pharmacist Sule ta godewa tawagar bisa ziyarar da suka kai tare da ba su tabbacin hadin kan DMCSA a duk lokacin da ake gudanar da aikin tantancewa.

 

KHADIJAH ALIYU/Wababe

Labarai

Labarai10 hours ago

Tinubu Ya Nada Ibrahim Masari a Matsayin Mai Ba Shi Shawara Kan Harkokin Siyasa

Daga Bello Wakili Shugaban Ƙasa Bola Tinubu  ya naɗa Ibrahim Aminu Masari a matsayin Mai ba shi Shawara na Musamman...

Labarai11 hours ago

Kungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Wata ƙungiyar al’umma mai suna Hadejia Advocacy ta yaba wa Gwamnan  Jigawa, Umar Namadi, kan yadda...

Labarai17 hours ago

Ramadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu

Daga Yusuf Zubairu Kauru Sarkin Kauru da ke Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u Shehu Usman, ya yi kira da a...

Labarai18 hours ago

Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin  Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar...

Labarai2 days ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi2 days ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai2 days ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai3 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai4 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Mafi Shahara