Connect with us

Labarai

‘Yansanda Sun Yi Kame A Sakkwato

Published

on

 

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da hannu a harin kasuwar kauyen Sokoto da ya yi sanadin mutuwar mutane shida a wani kauye da ake kira Kiri da ke karamar hukumar Gada a jihar Sokoto.

 

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto, ASP Ahmad Rufa’i ne ya bayyana haka ga wakilinmu a wata tattaunawa ta wayar tarho.

 

A wata hira da Rediyon Najeriya ta wayar tarho, PPRO na rundunar ‘yan sandan jihar ASP Ahmad Rufa, ya ce an kama wadanda ake zargin dauke da shanu 3 da wata bindiga kirar gida.

 

A cewarsa, wadanda ake zargin ‘yan asalin Sabon garin Dole ne a karamar hukumar Goronyo a jihar Sokoto kuma duk sun amsa laifin da suka aikata.

 

A wani labarin kuma, rundunar ‘yan sandan ta ce tana gudanar da bincike kan zargin kashe wani da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da wasu ’yan daba suka kashe a tsohon filin jirgin sama na jihar Sakkwato.

 

Wasu majiyoyi a yankin sun ce wani harin da aka kai ya kai ga halaka wani da ake zargin dan fashi da makami ne.

 

Majiyar wadda ba ta son a bayyana sunansa ta ce ‘yan sandan sun fara kame wadanda ake zargi da hannu a ciki da suka kashe wanda ake zargin dan fashi da makami ne.

 

Kakakin ‘yan sandan ya ce shugabannin al’ummar yankin sun tattauna da hukumar ‘yan sanda kuma ‘yan sandan za su dauki matakin da ya dace bayan kammala bincike kan lamarin.

 

NASIR MALALI/Wababe

Labarai

Labarai2 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai2 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai2 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi2 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai3 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai3 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai4 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai4 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai4 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara