Connect with us

Labarai

An Gina Riyojin Burtsatse ga yankunan da aka kai hari a Jihar Plateau

Published

on

Asusun tallafaws wadanda wata masifa ta fadawa ya gina riyojin burtsatse ga wasu al’ummomi da rikicin baya bayan nan ya Shafa a jihar Plateau.

Mai bada shawara na musamman ga shugaban asusun Janar Theophilus Danjuma, Mrs Toyosi Akenrele-Ogunsiji tace asusun na da manufar yaye wahalhalun da ‘yan Nijeriya suke sha.

Wakilinmu Josiah Buzun na dauke da karin bayani daga Jos.

Hare haren da aka rika kaiwa wasu kananan hukumomin jihar Plateau yayi sanadiyar jama’a da dama suka rasa kayyakin more rayuwarsu.

Wannan ne dalilin da ya sa asusun tallafawa wadanda masifa ta Shafa karlashin jagorancin Janar Theophilus Danjuma ya tona riyojin burtsatse don samarda ruwan sha ga al’umma.

An gina wadannan riyojin masu aiki da hasken Rana ga al’ummomin Doruwa, Babuje da Gassa a karamar hukumar Barikin Ladi, Sai Kuma a Ariri dake karamar hukumar Bassa da Kuma al’ummomin Sop dake tsalleken dogo a karamar hukunar Riyom.

Mrs. Akenrele Ogunsiji da ta wakilci shugabar asusun wajen bude wadannan ayukkan, tace mutane na bukatar tsaftaccen ruwan sha da wasu kayyayakin more rayuwa, don haka suke fara raba hatsi da Kuma kayan koyarwa da Kuma tallafawa don karfafa jama’a su dogara da kansu.

Mrs. Akenrele Ogunsiji tayi bayanin cewa, duk Wanda ke musu aiki da ya kasa gabatar da shi yanda ya dace zasu hukunta shi.

Shi kuma babbar daraktan asusun Farfesa Nana Tanko tace wajibi kowa ya amfana da wadannan riyojin da aka tona.

A jawabinsa babban sakataren hukumar bada agajin gaggauwa na jihar Plateau Mr. Sunday Abubu ya hori wadanda suka amfana da wannan aikin su kula da shi sosai.

Shugaban al’ummar Gassa da ke karamar hukunar Barikin Ladi James Toma ya godewa wannan asusun da shugabansa Janar Theophilus Danjuma saboda sanya farin cikin a tsakanin talakawan kasan Nan.

Wadanda suka amfana da shirin bayan yabon wannan asusun sun kuma bayyana imanin cewa wannan aikin zai taimaka wajen samar da ruwansha mai tsafta tare da kawarda cutuka da ake samu daga ruwa tare da fatan za a Sami Karin irin wannan aikin.

Josiah/Shafii Wababe

Labarai

Labarai10 hours ago

Tinubu Ya Nada Ibrahim Masari a Matsayin Mai Ba Shi Shawara Kan Harkokin Siyasa

Daga Bello Wakili Shugaban Ƙasa Bola Tinubu  ya naɗa Ibrahim Aminu Masari a matsayin Mai ba shi Shawara na Musamman...

Labarai11 hours ago

Kungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Wata ƙungiyar al’umma mai suna Hadejia Advocacy ta yaba wa Gwamnan  Jigawa, Umar Namadi, kan yadda...

Labarai17 hours ago

Ramadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu

Daga Yusuf Zubairu Kauru Sarkin Kauru da ke Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u Shehu Usman, ya yi kira da a...

Labarai18 hours ago

Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin  Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar...

Labarai2 days ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi2 days ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai2 days ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai3 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai4 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Mafi Shahara