Labarai
Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata
Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da kamfanoni masu zaman kansu su hada kai wajen samar da yanayin da zai bai wa mata da ’yan mata damar cimma burinsu.
A sakon da ta fitar domin bikin Ranar Mata ta Duniya ta 2026, Hajiya Huriyya ta ce taken bana “Give to Gain” na nuna muhimmancin zuba jari a kan mata ta hanyar ba su ilimi, horo da damar samun albarkatu.
Ta ce mata na taka muhimmiyar rawa wajen gina iyali, karfafa al’umma da kuma bunkasa tattalin arziki da zamantakewa.
Ta kuma tabbatar da cewa ofishinta zai ci gaba da tallafa wa shirye-shiryen da ke taimaka wa mata da ’yan mata musamman a bangarorin lafiya, ilimi, sana’o’i da walwalar jama’a.
Hajiya Huriyya ta kuma bukaci mata a Zamfara su ci gaba da jajircewa wajen ba da gudunmawa ga ci gaban jihar, tare da amfani da sauran kwanakin Ramadan wajen yi wa Zamfara da Najeriya addu’ar zaman lafiya da ci gaba.
Aminu Dalhatu/Gusau
-
Labarai6 days agoAna Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
-
Labarai6 days agoJam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano
-
Labarai5 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoGwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya
-
Labarai4 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai4 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara
