Connect with us

Ilimi

Unimaid Ta Karbi Bakuncin Taro Karo Na Farko Akan Rashin Tsaro

Published

on

An bude taron kwanaki biyu na kasa da kasa kan matsalar tsaro da sake tsugunar da jama’a da sake gina kasar a birnin Maiduguri na jihar Borno.

Taron mai taken “Rashin tsaro, Sake Ginawa, Gyara da Matsugunni a Yankin Tafkin Chadi” wanda Tsangayar Nazarin Tarihi da Dabarun mulkin na Jami’ar Maiduguri ne suka shirya, wanda ya samu halartar mahalarta daga ciki da wajen kasar nan.

A nasa jawabin tsohon babban hafsan sojin kasa Laftanar Janar Tukur Buratai (mai ritaya) ya jaddada cewa akwai bukatar Najeriya ta mai da hankali sosai kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi da yankin Sahel sakamakon rashin zaman lafiya da yankin ke fuskanta.

Janar Buratai ya ba da shawarar yin garambawul ga ‘yan sandan Najeriya a fannonin fasaha, horarwa, kwarewa da kuma nagarta don tunkarar kalubalen tsaro da ke kunno kai a yankin.

Ya kuma yi kira da a maido da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi domin tabbatar da ci gaba mai dorewa a matakin farko.

Buratai ya kara da cewa, “Bawa kananan hukumomi damar daukar nauyin ayyukansu na ci gaba yana da matukar muhimmanci wajen samar da dorewar zaman lafiya da dorewar yankin, wanda a karshe zai kai ga samar da al’umma mai wadata da daidaito.” Inji Buratai.

Shugaban Jami’ar Maiduguri, Farfesa Aliyu Shugaba ya ce maharan sun kai wa makarantar hari, amma duk da haka ta kasance a bude ko da a lokacin da rikici ya barke.

Ya kuma yi kira ga mahalarta taron da su yi nazari sosai kan abubuwan tarihi kamar rikicin Boko Haram tare da samar da ingantattun hanyoyin da al’umma ke bukata.

“Na yi farin ciki da cewa Tsangayar Nazarin Tarihi da Dabaru tsaro ta shirya wannan taro na farko na kasa da kasa domin jawo hankulan malamai game da rikicin Boko Haram ta fuskar tarihi.” Shugaba yace.

Shugaban Jami’ar Sojojin Najeriya, Farfesa Kyari Mohammed ya yi kira da a samar da tsarin shari’a na kasa don tafiyar da ficewar jama’a tare da sake shigar da masu tayar da kayar baya a cikin al’umma.

Kimanin kasidun ilimi 40 ne za a gabatar da su yayin taron.

Cov/Dauda/Wababe

Labarai

Labarai11 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi11 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai11 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai13 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara