Connect with us

Labarai

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 12 A Sambisa, Zamfara Da Katsina

Published

on

Dakarun Sojin Najeriya sun hallaka ‘yan ta’addan Boko Haram 12 a dajin Sambisa da ke Jihar Borno, da kuma wasu mahara a Zamfara da Katsina.

Daraktan hulda da jama’a na rundunar, Manjo Janar Onyema Nwachukwu ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja.

Nwachukwu ya ce sojojin sun yi galaba a kan ‘yan ta’addan a dajin Sambisa, inda suka kashe guda takwas a wani artabu da suka yi.

Ya ce a yayin farmakin, an yi kazamin artabu a tsakaninsu wanda ya yi sanadin kashe ‘yan ta’adda, sannan sauran suka tsere.

A cewarsa, sojojin sun kwato bindigogi guda biyar, babura biyu da kuma kayan abinci da dama daga hannun ‘yan ta’addan.

Nwachukwu ya ce a wani samame da sojoji suka kai Karamar Hukumar Kankara ta Jihar Katsina, sun kashe ’yan ta’adda biyu.

Kazalika, ya ce sun kwato bindigogi kirar AK-47 guda uku, harsashi guda 57 da kuma sauran makamai.

Ya kara da cewa sojojin sun kuma ceto wani mutum, tare da kone baburan ’yan ta’addan guda biyu da kuma kone sansaninsu a karamar hukumar.

Ya ce sojojin sun kuma fatattaki ’yan ta’adda a kauyukan Dandalla, Madada, Dogon Karfe, Hayi, Gobirawan da Kango Kuyambana a kananan hukumomin Gusau da Maru a Jihar Zamfara.

A cewarsa, sojojin sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu tare da kwato bindiga kirar AK-47 guda daya, bindigogi kirar gida guda uku, harsasai, da kuma babur guda daya.

Har wa yau, Nwachukwu ya ce a ranar Lahadi sojojin sun kai samame tare da lalata masana’antar kera bindigogi ta IPOB da ke yankin Ekoli Edda da Amagwu Ohafia a Jihar Ebonyi da Jihar Abiya.

Kazalika, ya jaddada aniyar rundunar na ci gaba da kai samame da hare-hare domin dakile ayyukan ’yan ta’adda a fadin Najeriya.

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara