Connect with us

Labarai

Dakarun Isra’ila sun lakaɗa wa likitoci duka a Gaza

Published

on

Falasɗinawa ma’aikatan lafiya a Gaza sun shaida wa BBC cewa dakarun Isra’ila sun rufe musu idanu da kyallaye, an tsare su kuma an tilasta musu tuɓe kayansu, yayin da aka yi ta lakaɗa musu duka a lokacin da sojin suka kai samame asibitin da suke aiki a watan Fabrairun da ya wuce.

Ahmed Abu Sabha, wani likita ne a asibitin Nasser, ya bayyana yadda sojin Isra’ilan suka tsare shi na tsawon mako guda, aka cinna mishi karnunka kuma suka karya masa hannu.

Abin da ya faru gare shi ya zo daidai da wasu likitocin biyu waɗanda suka nemi a sakaya sunayensu saboda tsoron ɗaukar matakan ramuwar gayya a kansu.

Sun shaida wa BBC cewa an muzanta su sun dake su, sun kwara musu ruwan sanyi kuma sun sanya su tsuguno mara daɗi na tsawon lokaci.

Haka kuma sun ce an tsare su na tsawon kwanaki kafin a sake su.

BBC ta bayyana wa ma’aikatar tsaron Isra’ila zarge-zargensu, amma bata mayar da martani kai tsaye kan tambayoyin da aka yi mata ba game da abubuwan da suka ce an yi musu, haka zalika bata musanta azaftarwar ba a ɗaiɗai kunsu, amma ta musanta cutar da wani jami’in lafiya a yaƙin da take yi.

Sun ce “duk wani cin zarafi na waɗanda ake tsare da su ya saɓawa umarnin ma’aikatar tsaron ta IDF, kuma don haka an haramta hakan”.

Labarai

Labarai9 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara