Falasɗinawa ma’aikatan lafiya a Gaza sun shaida wa BBC cewa dakarun Isra’ila sun rufe musu idanu da kyallaye, an tsare su kuma an tilasta musu tuɓe kayansu, yayin da aka yi ta lakaɗa musu duka a lokacin da sojin suka kai samame asibitin da suke aiki a watan Fabrairun da ya wuce.
Ahmed Abu Sabha, wani likita ne a asibitin Nasser, ya bayyana yadda sojin Isra’ilan suka tsare shi na tsawon mako guda, aka cinna mishi karnunka kuma suka karya masa hannu.
Abin da ya faru gare shi ya zo daidai da wasu likitocin biyu waɗanda suka nemi a sakaya sunayensu saboda tsoron ɗaukar matakan ramuwar gayya a kansu.
Sun shaida wa BBC cewa an muzanta su sun dake su, sun kwara musu ruwan sanyi kuma sun sanya su tsuguno mara daɗi na tsawon lokaci.
Haka kuma sun ce an tsare su na tsawon kwanaki kafin a sake su.
BBC ta bayyana wa ma’aikatar tsaron Isra’ila zarge-zargensu, amma bata mayar da martani kai tsaye kan tambayoyin da aka yi mata ba game da abubuwan da suka ce an yi musu, haka zalika bata musanta azaftarwar ba a ɗaiɗai kunsu, amma ta musanta cutar da wani jami’in lafiya a yaƙin da take yi.
Sun ce “duk wani cin zarafi na waɗanda ake tsare da su ya saɓawa umarnin ma’aikatar tsaron ta IDF, kuma don haka an haramta hakan”.