Connect with us

Labarai

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 12 A Sambisa, Zamfara Da Katsina

Published

on

Dakarun Sojin Najeriya sun hallaka ‘yan ta’addan Boko Haram 12 a dajin Sambisa da ke Jihar Borno, da kuma wasu mahara a Zamfara da Katsina.

Daraktan hulda da jama’a na rundunar, Manjo Janar Onyema Nwachukwu ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja.

Nwachukwu ya ce sojojin sun yi galaba a kan ‘yan ta’addan a dajin Sambisa, inda suka kashe guda takwas a wani artabu da suka yi.

Ya ce a yayin farmakin, an yi kazamin artabu a tsakaninsu wanda ya yi sanadin kashe ‘yan ta’adda, sannan sauran suka tsere.

A cewarsa, sojojin sun kwato bindigogi guda biyar, babura biyu da kuma kayan abinci da dama daga hannun ‘yan ta’addan.

Nwachukwu ya ce a wani samame da sojoji suka kai Karamar Hukumar Kankara ta Jihar Katsina, sun kashe ’yan ta’adda biyu.

Kazalika, ya ce sun kwato bindigogi kirar AK-47 guda uku, harsashi guda 57 da kuma sauran makamai.

Ya kara da cewa sojojin sun kuma ceto wani mutum, tare da kone baburan ’yan ta’addan guda biyu da kuma kone sansaninsu a karamar hukumar.

Ya ce sojojin sun kuma fatattaki ’yan ta’adda a kauyukan Dandalla, Madada, Dogon Karfe, Hayi, Gobirawan da Kango Kuyambana a kananan hukumomin Gusau da Maru a Jihar Zamfara.

A cewarsa, sojojin sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu tare da kwato bindiga kirar AK-47 guda daya, bindigogi kirar gida guda uku, harsasai, da kuma babur guda daya.

Har wa yau, Nwachukwu ya ce a ranar Lahadi sojojin sun kai samame tare da lalata masana’antar kera bindigogi ta IPOB da ke yankin Ekoli Edda da Amagwu Ohafia a Jihar Ebonyi da Jihar Abiya.

Kazalika, ya jaddada aniyar rundunar na ci gaba da kai samame da hare-hare domin dakile ayyukan ’yan ta’adda a fadin Najeriya.

Labarai

Labarai7 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara