Labarai
Shugaba Tinubu Ya Taka Rawar Gani Sosai — Buhari
Tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, ya ce magajinsa, Bola Ahmed Tinubu, yana taka rawar gani sosai tun bayan hawansa mulki watanni tara da suka wuce.
Tsohon shugaban kasar, ya ce Tinubu ya taka rawar gani idan aka yi la’akari da yanayin da ake ciki, amma ya ce Najeriya kasa ce mai wuyar sha’ani.
Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban Hukumar Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi da wasu jami’an hukumar a Daura a ranar Lahadi.
Tinubu dai ya fuskanci suka kan wasu daga cikin manufofin da ya bijiro da su game da tattalin arziki da suka hada da cire tallafin man fetur.
Buhari ya ce yana da matukar wahala ga ‘yan kasar su iya jure matsin tattalin arziki da ake fama da shi, sai dai ya ce yana goyon bayan manufofi da tsare-tsaren gwamnati mai ci.
“Na gode kwarai da ziyararku. Na yaba sosai. Ina kyautata zaton Tinubu ya yi kokari sosai zuwa yanzu,” in ji Buhari.
“Najeriya tana da sarkakiya sosai. Hakika, da wuya wani ya iya wani abun a zo a gani.”
Har wa yau, shugaban na Kwatsam ya ziyarci mai martaba Sarkin Daura, Dokta Farouk Umar Farouk.
A yayin ziyarar, Adeniyi ya ce “Wannan mataki na doka ya bai wa hukumar Kwastam damar fadada manufofin samar da kudaden shiga da kuma saukaka harkokin kasuwanci, haka kuma ya taimaka sosai ga ci gaban tattalin arzikin Najeriya,” in ji Adeniyi.
Idan dai ba a manta ba, wannan ba shi ne karon farko da Buhari ya yi furuci kan wahalar shugabanci da Najeriya ta ke da shi ga masu rike da akalar jagoranci ba.
“’Yan Najeriya na da wahala wajen shugabanci. Mutane ne da suka san hakkinsu. Suna ganin ya kamata su kasance a wajen ba kai ba. Don haka, suna lura da kusan kowane mataki da aka dauka. Kuma dole ne ka jajirce dare da rana don tabbatar da cewa ka yi kokari sosai,” in ji Buhari.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United