Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu Ya Taka Rawar Gani Sosai — Buhari

Published

on

Tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, ya ce magajinsa, Bola Ahmed Tinubu, yana taka rawar gani sosai tun bayan hawansa mulki watanni tara da suka wuce.

Tsohon shugaban kasar, ya ce Tinubu ya taka rawar gani idan aka yi la’akari da yanayin da ake ciki, amma ya ce Najeriya kasa ce mai wuyar sha’ani.

Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban Hukumar Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi da wasu jami’an hukumar a Daura a ranar Lahadi.

Tinubu dai ya fuskanci suka kan wasu daga cikin manufofin da ya bijiro da su game da tattalin arziki da suka hada da cire tallafin man fetur.

 

Wadannan tsare-tsare da sauransu sun haifar da hauhawar farashin kayayyaki, tabarbarewar tattalin arziki, da faduwar darajar Naira, wanda hatta a ‘yan kwanakin nansai da aka yi zanga-zanga a fadin kasar nan.

 

Buhari ya ce yana da matukar wahala ga ‘yan kasar su iya jure matsin tattalin arziki da ake fama da shi, sai dai ya ce yana goyon bayan manufofi da tsare-tsaren gwamnati mai ci.

“Na gode kwarai da ziyararku. Na yaba sosai. Ina kyautata zaton Tinubu ya yi kokari sosai zuwa yanzu,” in ji Buhari.

“Najeriya tana da sarkakiya sosai. Hakika, da wuya wani ya iya wani abun a zo a gani.”

 

A nasa jawabin, Adeniyi ya gode wa tsohon shugaban kasar kan rawar da ya taka wajen tabbatuwar Dokar Hukumar Kwastam (NCS) ta 2023.

 

Har wa yau, shugaban na Kwatsam ya ziyarci mai martaba Sarkin Daura, Dokta Farouk Umar Farouk.

A yayin ziyarar, Adeniyi ya ce “Wannan mataki na doka ya bai wa hukumar Kwastam damar fadada manufofin samar da kudaden shiga da kuma saukaka harkokin kasuwanci, haka kuma ya taimaka sosai ga ci gaban tattalin arzikin Najeriya,” in ji Adeniyi.

Idan dai ba a manta ba, wannan ba shi ne karon farko da Buhari ya yi furuci kan wahalar shugabanci da Najeriya ta ke da shi ga masu rike da akalar jagoranci ba.

 

A watan Nuwamban 2023, yayin wata hira da gidan talabijin na Najeriya (NTA), Buhari ya ce Najeriya tana da wahalar shugabanci.

 

“’Yan Najeriya na da wahala wajen shugabanci. Mutane ne da suka san hakkinsu. Suna ganin ya kamata su kasance a wajen ba kai ba. Don haka, suna lura da kusan kowane mataki da aka dauka. Kuma dole ne ka jajirce dare da rana don tabbatar da cewa ka yi kokari sosai,” in ji Buhari.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai7 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara