Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu Ya Jajantawa Al’ummar Jihar Neja Bisa Iftila’in Fashewar Tankar Mai

Published

on

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana alhininsa kan fashewar tankar mai da ta yi sanadin mutuwar mutane sama da 80 tare da jikkata wasu da dama a jihar Neja.

Wata sanarwar mai dauke da sa hannun mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Mista Bayo Onanuga, ta ce shugaba TTinubu ya yi jimamin afkuwar lamarin, ya kuma jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, da kuma gwamnati da al’ummar jihar Neja.

Shugaban ya bayyana takaicinsa duba da yadda mafi yawan wadanda lamarin ya rutsa da su, masu kokarin dibar mai ne daga tankar man da ta fadi.

Shugaban ya bayar da umarnin ba da cikakkiyar kulawa ga wadanda suka jikkata, sannan ya umarci hukumomin tsaro da na kiyaye hadurra da su aiwatar da matakan dakile afkuwar irin wannan lamari.

Ya shawarci jama’a da su yi taka-tsan-tsan tare da kaucewa tunkarar wuraren da aka samu irin wadannan hadurra, musamman ma na motocin da ke dauke da man fetur.

Shugaban ya umarci hukumar wayar da kan jama’a ta kasa da ta kaddamar da gangamin wayar da kan jama’a game da munanan hadurra da kuma illolin da ke tattare da debo man fetur daga tankar mai.

 

Daga Bello Wakili

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara