Connect with us

Ilimi

Gwamna Namadi Tare Da Hadin Gwiwar Kasar Qatar Sun Samar Da Cibiyar Bunkasa Ilimi A Jigawa

Published

on

Gwamna Mallam Umar Namadi ya kaddamar da Cibiyar Al’amuran  Addinin Musulunci a kauyen Babbar Riga dake karamar hukumar Malam-Madori a jihar Jigawa.

Cibiyar wacce aka ginata tare da  hadin gwiwar wata kungiyar Agaji ta kasar Qatar mai zaman kanta da kuma gwamnatin jihar Jigawa, an tsara shi ta ne  domin kawo sauyi ga al’umma ta kyautata rayuwarsu, da samar da ingantaccen ilimi.

Sabuwar cibiyar da aka kaddamar ta kunshi rukunin gidaje, da ginin makaranta na zamani, da masallaci, wadanda za su samar da yanayi mai kyau na koyo da ci gaban al’umma.

Wannan shiri ya jaddada kudirin gwamnatin jihar Jigawa na bunkasa ilimi da inganta rayuwar al’umma.

A yayin bikin, Gwamna Namadi ya yabawa kungiyar Qatar Charity bisa sadaukarwar da ta yi, sannan ya bukaci a ci gaba da hada kai don fadada irin wadannan ayyuka a fadin jihar Jigawa.

Ya sanar da cewa hukumar kula da ilimin bai daya ta jihar (SUBEB) za ta kula da wurin domin tabbatar da kulawar da ta dace, tare da samar da  malamai da sauran kayayyakin aiki a makarantar.

 

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan jihar Jigawa, Hamisu Mohammed Gumel ya fitar, ya ce bikin kaddamarwar ya samu halartar manyan baki da suka hada da jakadan Qatar a Najeriya, Ali Bin Ghanem Al-Hajri; da Daraktan kungiyar agaji ta Qatar, Hamdi Abdou.

 

Sauran sun hada da Darakta-Janar na Hukumar Bunkasa Fasahar Sadarwa ta Kasa (NITDA), Kashifu Abdullahi; da  Sarkin Hadejia, Alhaji Adamu Abubakar Maje; da sauran fitattun shugabanni da sauran al’umma.

Kungiyar Qatar Charity ta mikawa gwamnatin jihar Jigawa ginin a hukumance, inda al’ummar yankin suka fara amfani da ita.

Mista Hamdi Abdou, daraktan kungiyar agaji na kasar, ya yabawa Gwamna Namadi bisa hangen nesa, tare da yin alkawarin ci gaba da kawo dauki a jihar Jigawa a wannan shekarar  ta 2025.

Wannan aiki na nuni da  cika alkawarin da Qatar Charity ta yi a lokacin da Gwamna Namadi ya ziyarci ofishinsu na Abuja a shekarar da ta gabata.

Da wannan hadin gwiwa, jihar Jigawa na ci gaba da kafa tarihi na hadin gwiwa mai ma’ana da nufin magance kalubalen ilimi da gidaje, da samar da ci gaba mai dorewa ga al’ummarta.

 

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai18 hours ago

Matasan Kauru Sun Yi Allah-wadai da Mulkin Ƙarfi, Sun Buƙaci Adalci da Haɗin Kai

  Daga Yusuf Zubairu Wata ƙungiyar matasa a Ƙaramar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna ta bayyana cewa shugabanci na bai-ɗaya...

Labarai2 days ago

Ma’aikatar Lafiya Ta Fara Daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa a Jigawa

Usman Muhammad Zaria  Ma’aikatar Lafiya ta kasa karkashin shirin kula da lafiya na SWAP ta fara aikin daukar Jami’an Kula...

Labarai1 week ago

Baragurbi a Aikin Jarida na Barazana ga Sahihancin Kafafen Yada Labarai – Shugaban NUJ-FRCN

Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen FRCN Kaduna, Kwamared Umar Adamu Sarkinfada, ya bayyana cewa mummunan aikin jarida...

Labarai2 weeks ago

Ƙaruwa a Shan Abubuwan Sha Masu Ƙara Ƙarfi na Haddasa Damuwar Lafiya a Kano

Abubuwan sha masu ƙara ƙarfi, waɗanda aka fi sani da energy drinks ko energizers, na ƙara samun karɓuwa a faɗin...

Labarai2 weeks ago

Shugaba Tinubu Ya Taya CPSO Usman Shugaba Murnar Cika Shekara 45 da Haihuwa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Kwamishinan ‘Yan Sanda, Usman Musa Shugaba, wanda shi ne Babban Jami’in Tsaron ‘Yan...

Labarai2 weeks ago

TSARO: Gwamnan Jihar Neja Ya Nuna Alhini Kan Harin ‘Yan Ta’adda a Al’ummomin Borgu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa kan harin ‘yan ta’adda da aka kai wa wasu...

Labarai2 weeks ago

Allah Ya Jikan Jarman Kauru Da Ke Jihar Kaduna

Mun sami labarin rasuwar tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Malam Suleiman Lawal Jarman Kauru. Malam Suleiman Lawal, mai shekaru...

Labarai2 weeks ago

Gwamnatin Kano Ta Faɗaɗa Damar Tattalin Arziki ga Mata da Masu Buƙata Ta Musamman

An kammala kasuwar baje kolin mata ta tsawon kwanaki huɗu, wadda Ma’aikatar Harkokin Mata, Yara da Masu Buƙata Ta Musamman...

Labarai2 weeks ago

Rundunar Tsaro Ta Haɗin Gwiwa Ta Hallaka ’Yan Bindiga 150

Rundunar tsaro ta haɗin gwiwa da ta ƙunshi Sojojin Nijeriya, Hukumar Tsaron Farin Ciki (DSS), ’Yan Sanda da sauran hukumomin...

Ilimi2 weeks ago

Gwamnatin Neja Ta Amince da Sake Buɗe Makarantun Gwamnati da Masu Zaman Kansu daga 12 ga Janairu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya amince da sake buɗe dukkan makarantun gwamnati da masu zaman kansu a faɗin...

Mafi Shahara