Connect with us

Labarai

Gwamnatin Neja Ta Haramtawa Motocin Da Suka Fito Daga Hanyar Maje Bin Gadar Dikko

Published

on

Gwamnatin Jihar Neja ta ba da umarnin hana motocin da suka  fito daga Maje hawa gadar Dikko.

Gwamnan jihar Mohammed Umar Bago ya ba da umarnin a lokacin da ya ziyarci wurin da wata tankar mai  ta yi  gobara a mahadar Dikko da ke karamar hukumar Gurara ta jihar Neja.

Gwamnan, wanda ya koka kan yadda wasu direbobi ke nuna halin ko-in-kula yayin tuki, ya ce ba a amince duk wata mota da ta fito daga Maje ta bi ta gadar Dikko ba, sai dai su bi karkashin gadar zagayo kan hanyarsu.

Ya kuma umurci babban kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta tarayya da ya kafa rundunar tsaro a yankin domin tabbatar da aiwatar da wannan umarni, yayin da ya yi kira ga kungiyoyin sufuri da abin ya shafa da su ba hukumar kiyaye hadurra ta kasa hadin kai.

Sai dai Gwamnan ya bayyana fashewar tankar mai da ta yi sanadin mutuwar mutane da dama a matsayin abin tausayi tare da gode wa Allah da lamarin bai kai ga al’ummar da ke makwabtaka da su ba.

Umar Bago ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta daukar matakin kammala aikin titin Minna zuwa Suleja domin jinkirin aikin hanyar yana haddasa asarar  rayuka da dukiyoyi.

Gwamnan ya godewa Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, da Hukumar Kashe Gobara, da Hukumar kiyaye hadurra ta kasa, da Kungiyar Sufuri ta Kasa (NURT) da sauran hukumomin da suka bayar da gudunmawa wajen kawo dauki ga  wadanda fashewartankarya rutsa da su.

Ya ce za a kara  tura likitoci daga asibitocin da ke Minna domin su taimaka wajen kula da wadanda suka jikkata da ke samun kulawa a  babban asibitin Suleja.

Daga Aliyu Lawal

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara