Connect with us

Labarai

Niger Ta Yi Umurnin Kama Duk Wanda Yake Yunkurin Tada Zaune Tsaye

Published

on

 

 

Gwamnatin Jihar Neja ta yi gargadin cewa daga yanzu duk wani matashi ko gungun jama’a da aka samu da hannu wajen tashe-tashen hankula da hana zaman lafiya a Minna babban birnin jihar da kewaye za a kama su.

 

Kwamishinan Tsaron Cikin Gida Birgediya Janar, Garba Abdullahi Mohammed wanda ya yi wannan gargadin a wata tattaunawa ta wayar tarho da Rediyon Najeriya a Minna ya ce gwamnatin jihar za ta ci gaba da hukunta duk wasu masu tada zaune tsaye.

 

Birgediya Janar Garba Abdullahi Mohammed ya ci gaba da bayanin cewa za a hukutan duk wani mutum ko maai girman sa da aka samu da yunkurin belin duk wani bata gari da aka kama.

 

Ya ce gwamnatin jihar ba za ta nade hannunta ba sannan ta bar miyagu su lalata rayuka da dukiyoyin ‘yan Nigeriya da ke gudanar da sana’o’insu na halal.

 

Kwamishinan yana mayar da martani ne game da tashe-tashen hankula da matasan suka yi a Minna musamman wanda ya faru kwanan nan inda aka kashe mutane biyu tare da jikkata wasu a wani turmutsitsi tsakanin kungiyoyin matasa biyu a Maotumbi da ke karamar hukumar Bosso a jihar Neja. .

 

Kwanaki uku da suka gabata wasu matasa da suka addabi yankin Fadikpe ne suka kashe wani ma’aikacin lafiya mai suna Umar a lokacin da suke dawowa daga aiki, inda suka ce hakan bai dace ba kuma ya shawarce su da su daina ko kuma su fuskanci fushin doka.

 

A halin da ake ciki dai an tsaurara matakan tsaro a yankunan da ake fama da tashin hankali da kuma wasu sassa na Minna babban birnin jihar domin ganin an fara samun tashe-tashen hankulan matasa, tada zaune tsaye da kuma nuna kyama.

 

KARSHEN ALIYU LAWAL/Wababe

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara