Connect with us

Labarai

NDLEA Ta Kama Sama Da Tan 2 Na Miyagun Kwayoyi Da Mutane 929 A Jihar Kwara

Published

on

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) reshen jihar Kwara, ta kama tan 2 da digo 6 na miyagun kwayoyi, tare da kama mutane 929 tsakanin watan Janairu zuwa Disamban wannan shekara.

Kwamandar hukumar ta NDLEA a jihar Kwara, Fatima Popoola ce ta bayyana hakan yayin da take yi wa manema labarai karin haske kan nasarorin da hukumar ta samu a Ilori.

Ta ce daga cikin wadanda ake zargin 839 maza ne yayin da 90 kuma mata ne.

Misis Popoola ta ce magungunan da aka gano sun hada da, tabar wiwi da kwayar Tramadol,  da diazapam, da  methamphetamine, da maganin tari na ruwa da hodar ibilis da sauransu.

Ta ce tabar wiwi da ke kan gaba a jerin kwayoyin ta kai nauyin kilogiram miliyan daya da rabi.

Ta yi nuni da cewa, yayin wani aikin hadin gwiwa da hukumar ta yi cikin gaggawa, ta kama masu shaye-shaye 185, wadanda aka fadakar da su illar shaye-shaye, tare da ba su shawarwari, aka kuma maida su ga iyalansu.

Misis Popoola ta ci gaba da cewa, hukumar  tare da hadin gwiwar gwamnatin jihar, ta fara aiwatar da shirin gwajin magunguna kan sabbin dalibai 261 na jami’ar jihar Kwara.

Kwamandar hukumar ta NDLEA ta yabawa kokarin gwamnatin jihar da sauran jami’an tsaro bisa tallafawa ayyukansu.

Ta shawarci iyaye da su kasance masu sa ido kan al’amuran  ‘ya’yansu don kaucewa tu’ammali da miyagun  mutane.

Misis Popoola ta bukaci gwamnatin jihar da ta taimaka wa hukumar da karin motocin aiki tare da kammala ginin cibiyar gyaran dabi’u domin saukaka ayyukansu.

Ta kuma yi kira ga jama’a da su taimaka wa hukumar da bayanai kan ayyukan masu safarar miyagun kwayoyi domin samun nasara.

 

Ali Muhammad Rabi’u

Labarai

Labarai18 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi18 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai19 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai20 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara