Labarai
Majalisar Wakilai Za Ta Gabatar Da Dokoki Biyar Don Gyara Bangaren Man Fetur
Majalisar Wakilai za ta gabatar da kudurori guda biyar da za su magance manyan kalubale da ke hana ingantaccen aiki a harkar man fetur ta kasa.
Shugaban kwamitin Majalisar kan Albarkatun Man Fetur, Alhaji Alhassan Ado Doguwa, ne ya bayyana hakan yayin wani taro na hadin gwiwa da kwamitin musamman kan matsalar satar danyen mai a Abuja.
Alhaji Alhassan Ado Doguwa ya ce kudurorin da ake shirin gabatarwa, za a gabatar da su ne tare da shugabannin kwamitocin biyu, kuma wani bangare ne na matakan dokoki don tallafawa kokarin gwamnati wajen kare kadarorin man fetur da gas da kuma dakile matsalar satar danyen mai.
Ya bayyana cewa daya daga cikin kudurorin na neman kafa Hukumar Kasa da za ta sami ikon dakile ayyukan masu lalata bututun mai da gurfanar da su , da kuma aikata wasu laifuka da suka shafi bangaren man fetur.
“Kwamitocin da duk Majalisar baki daya na matukar damuwa da karuwar rashin tsaro da ayyukan laifi a yankunan da ake hakar mai. Wannan mataki na majalisa wata hanya ce ta tallafa wa kokarin gwamnati wajen kare wadannan muhimman kadarorin kasa,” in ji Alhaji Ado Doguwa.
Har ila yau, Alhaji Ado Doguwa ya bayyana cewa daya daga cikin kudurorin da ke karkashin Kwamitin Albarkatun Man Fetur (Sashen Sama), wanda Kakakin Majalisar, Dr Abbas Tajuddeen, ke jagoranta, na neman kafa Hukumar da za ta kula da cire kayan aikin hakar mai da suka tsufa, matsala da ke da matukar muhimmanci ga al’ummomin da ke karbar bakuncin ayyukan man fetur da sauran masu ruwa da tsaki.
Salihu Tsibiri
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
