Connect with us

Labarai

Kungiyar ‘Yan Sintiri Ta Bayyana Rashin Goyon Bayanta Kan Kafa ‘Yan Sandan Jihohi

Published

on

Babban kwamandan Kungiyar ‘Yan sintiri ta Sakai ta kasa da aka fi sani da “Vigilante Group of Nigeria,” ya bayyana rashin goyon bayansu na kafa ‘Yansandan jihohi a Najeriya.

Babban kwamandan kungiyar Nebi Kaftin mai ritaya, Umar Bakori ya ce ba sa goyon bayan kafa Yansandan Jihohi a Najeriya, bayan da Kungiyar ta gabatar da gyare-gyare da ta ke so a yi a Kundin Tsarin Mulki ga kwamatin tsaro na Majalisar Wakilai a ranar Talatan nan.

Kaftin Bakori ya ce wannan yunkuri na kafa Yansandan Jihohi wata hanyace da ake amfani da ita wajen cinhanci da rashawa ta hanyar kwasar makudan kudade da sunan samar da tsaro.

Bakori ya ce Gwamnatin Taraiya ta kashe sama da Naira biliyan 13 don samar da Yansandan Al’umma amma hakan ya wuce babu wani canji da aka samu.

Ya bayar da misali da ikirarin Gwanonin Jihohin Katsina da Zamfara suka yi na cewa jihar Zamfarar ta kashe naira biliyan 10 kana jihar katsina ta kashe naira bilyan 17 domin samar da tsaro a jihohin su, sai dai acewarsa hakan bai samar da tsaron da a ke bukata ba a jihihin kawo yanzu

Ya ce Gwamnatin Jihar Ekiti ta kashe naira biliyan 1.4 da Jihar Ondo sun kashe naira biliyan 2 amma ba wata nasara.

In da ya ce a maimKon ha ka kamata ya yi gwamnonin su su tallafawa Kungiyar Vigilante don samar da tsaro a jihohin na su.

Kazalika ya kara da cewa tuni Kungiyar ta Vigilante na da mambobi sama da miliyan daya a Najeriya.

Kaftin Bakori ya ce mambobin su na da masaniya na wuraren da suke aiki kuma yan asalin yankin ne, sabo da haka suna da masaniya na lungu da sako na inda ma su laifi su ke, Sabo da haka suna taimakawa jami’an tsaro da bayanan sirri yadda ya da ce.

Ya ce Kungiyar ta su tana bukatar gwamnati ta amince da su kana ta basu kulawar da ta kamata ta hanyar basu tallafi na kudade a zama wani mataki na karfafa mu su gwiwa na cigaba da yin abun da suka sa kansu sama da shekaru 30 da suka gabata.

Shugaban ya bukaci Gwamnati ta samar da wata cibiya da za ta rinka bawa Yan Vigilante horo da Tsare-tsare da Dokoki don kyautata aikin su ta re da samar musu da kayan aiki da zai taimaka wajen samun nasarar aikin da su ke yi na rabbatar da tsaro a kasa.

Kwamandan ya nuna jin dadi na yadda Sojoji su ke basu hadin kai da goyon bayan ta yin aiki tare da juna, wanda hakan ya haifar da nasarori wajen kubutar da ‘Yan makarantar da aka yi garkuwa da su a Kuriga da Chibock da sauran wurare makamanta.

 

COV/Bashir M

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara