Labarai
Kungiyar ‘Yan Sintiri Ta Bayyana Rashin Goyon Bayanta Kan Kafa ‘Yan Sandan Jihohi
Babban kwamandan Kungiyar ‘Yan sintiri ta Sakai ta kasa da aka fi sani da “Vigilante Group of Nigeria,” ya bayyana rashin goyon bayansu na kafa ‘Yansandan jihohi a Najeriya.
Babban kwamandan kungiyar Nebi Kaftin mai ritaya, Umar Bakori ya ce ba sa goyon bayan kafa Yansandan Jihohi a Najeriya, bayan da Kungiyar ta gabatar da gyare-gyare da ta ke so a yi a Kundin Tsarin Mulki ga kwamatin tsaro na Majalisar Wakilai a ranar Talatan nan.
Kaftin Bakori ya ce wannan yunkuri na kafa Yansandan Jihohi wata hanyace da ake amfani da ita wajen cinhanci da rashawa ta hanyar kwasar makudan kudade da sunan samar da tsaro.
Bakori ya ce Gwamnatin Taraiya ta kashe sama da Naira biliyan 13 don samar da Yansandan Al’umma amma hakan ya wuce babu wani canji da aka samu.
Ya bayar da misali da ikirarin Gwanonin Jihohin Katsina da Zamfara suka yi na cewa jihar Zamfarar ta kashe naira biliyan 10 kana jihar katsina ta kashe naira bilyan 17 domin samar da tsaro a jihohin su, sai dai acewarsa hakan bai samar da tsaron da a ke bukata ba a jihihin kawo yanzu
Ya ce Gwamnatin Jihar Ekiti ta kashe naira biliyan 1.4 da Jihar Ondo sun kashe naira biliyan 2 amma ba wata nasara.
In da ya ce a maimKon ha ka kamata ya yi gwamnonin su su tallafawa Kungiyar Vigilante don samar da tsaro a jihohin na su.
Kazalika ya kara da cewa tuni Kungiyar ta Vigilante na da mambobi sama da miliyan daya a Najeriya.
Kaftin Bakori ya ce mambobin su na da masaniya na wuraren da suke aiki kuma yan asalin yankin ne, sabo da haka suna da masaniya na lungu da sako na inda ma su laifi su ke, Sabo da haka suna taimakawa jami’an tsaro da bayanan sirri yadda ya da ce.
Ya ce Kungiyar ta su tana bukatar gwamnati ta amince da su kana ta basu kulawar da ta kamata ta hanyar basu tallafi na kudade a zama wani mataki na karfafa mu su gwiwa na cigaba da yin abun da suka sa kansu sama da shekaru 30 da suka gabata.
Shugaban ya bukaci Gwamnati ta samar da wata cibiya da za ta rinka bawa Yan Vigilante horo da Tsare-tsare da Dokoki don kyautata aikin su ta re da samar musu da kayan aiki da zai taimaka wajen samun nasarar aikin da su ke yi na rabbatar da tsaro a kasa.
Kwamandan ya nuna jin dadi na yadda Sojoji su ke basu hadin kai da goyon bayan ta yin aiki tare da juna, wanda hakan ya haifar da nasarori wajen kubutar da ‘Yan makarantar da aka yi garkuwa da su a Kuriga da Chibock da sauran wurare makamanta.
COV/Bashir M
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
