Connect with us

Ilimi

Kungiyar ASUU Shiyar Sokoto Ta Bi Sahun Sauran Takwarorinta Game Da Barazanar Fara Yajin Aiki

Published

on

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta sanar da shirin shiga yajin aikin gargadi ga Gwamnatin Tarayya.

Da yake jawabi a taron manema labarai a Sokoto, Shugaban ASUU na yankin Sokoto, Farfesa Abubakar Sabo, ya ce wannan mataki ya biyo bayan gazawar gwamnati wajen magance manyan bukatun kungiyar tun da dadewa, yana mai gargadin cewa harkokin karatu a jami’o’in Najeriya za su tsaya cak, sakamakon yajin aiki a duk fadin kasa.

Farfesa Abubakar Sabo ya zargi gwamnati da yaudara da kuma sakaci ga bangaren ilimi.

Ya bayyana cewa kungiyar ta daina yarda da alkawuran gwamnati, yana mai cewa abin da ka iya dawo da amincewa shi ne daukar matakin gaggawa, kuma ingantattun, domin kaucewa durkushewar jami’o’in gwamnati.

Rediyon Najeriya ya ruwaito  cewa daya daga cikin matsalolin da ASUU ke adawa da shi, shi ne tsarin rancen ma’aikata da gwamnati ta gabatar. Kungiyar ta ce malaman jami’a ba sa bukatar rance, abin da suke bukata shi ne tsarin albashi mai inganci.

Yayin da yake yabawa da dakatar da kafa sabbin jami’o’i ba tare da tsari ba, ya ce ASUU ta gargadi gwamnati kan yadda ake yawaita kafa makarantu marasa cikakken shiri, tana mai cewa hakan na iya kawo cikas ga ci gaban bangaren ilimi.

A cewar Farfesa Sabo, har yanzu malaman jami’a har yanzu na bin albashin watanni uku da rabi da ba a biya su ba.

Ya kara da cewa akwai wasu matsalolin da ba a magance ba ciki har da bashin karin girma daga 2018 zuwa 2024 a Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sokoto; rashin tabbatar da dokar kafa Jami’ar Tarayya Gusau; rashin sakin kudi don fara aiki  jami’o’in Birnin Kebbi da Zuru; da kuma rashin kafa majalisar gudanarwa a Jami’ar Ilimi ta Shehu Shagari, Sokoto.

 

Daga Nasiru Malali 

 

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara