Ilimi
Jami’ar Bayero Ta Bayyana Alhininta Bisa Kisan Gillar Wani Dalibinta
Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta bayyana alhinita kan kisan gilla da aka yi wa Umar Abdullahi Hafizi, dalibi da ke matakin karatu na 3 a Sashen Ilimin Zamantakewa (Sociology), wanda wasu masu kwacen waya suka daba wa wuka har lahira a gidansa da ke unguwar Dorayi a ƙaramar hukumar Gwale.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Hulɗa da Jama’a na jami’ar, Malam Lamara Garba, ya fitar, wacce aka rabawa manema labarai.
A cewarsa, kodayake lamarin ya faru ne a wajen harabar jami’ar, shugabannin BUK sun jaddada cewa suna kokari wajen tabbatar da tsaron ɗalibansu.
Shugaban Jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya bayyana wannan lamari a matsayin babban rashi da ya girgiza al’ummar jami’ar, tare da mika ta’aziyyarsa ga iyalan mamacin, abokansa da ɗaliban jami’ar baki ɗaya.
Farfesa Abbas ya ce jami’ar na aiki kafada da kafada da hukumomin tsaro domin tabbatar da cewa waɗanda suka aikata wannan danyen aiki sun fuskanci hukunci.
Daga cikin matakan gaggawa da jami’ar ta ɗauka, sun haɗa da jigilar gawar mamacin zuwa garinsu na Zariya a Jihar Kaduna domin yi masa jana’iza bisa tsarin Musulunci.
BUK ta kuma shawarci ɗalibai da su zauna lafiya da yin taka-tsantsan, tare da kira ga jama’a da su taimaka wa jami’an tsaro da bayanan da za su iya taimaka wa binciken da ake ci gaba da yi.
Jami’ar Bayero ta yi addu’ar Allah ya jikan Umar Abdullahi Hafizi, ya kuma bai wa iyalansa juriyar wannan babban rashi.
Daga Khadijah Aliyu
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
