Labarai
Hadarin Jirgin Ruwa A Karamar Hukumar Borgu Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 29
An gano gawarwaki 29, yayin da aka ceto mutane 50 daga wani hadarin jirgin ruwa da ya auku a kauyen Gausawa na yankin Malale a karamar hukumar Borgu ta jihar Neja.
Lamarin ya faru ne ranar Talata da misalin ƙarfe 11 da rabi na safe, lokacin da jirgin ruwan da ke ɗauke da mutane 90 ciki har da mata da yara, ya nutse.
Matafiyan sun taso ne daga Tugan Sule da ke yankin Shagunu a kan hanyarsu ta zuwa Dugga domin yin ta’aziyya.
Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya danganta hatsarin da ɗaukar mutane fiye da ƙima da kuma karo da tushen itace a cikin ruwa, inda ya ce har yanzu ana ci gaba da neman mutane biyu daga cikin su.
A halin yanzu dai, ana ci gaba da aikin ceto da bincike domin gano sauran mutanen da ba a same su ba.
Daga AliyuLawal
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
