Connect with us

Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Sayo Motoci Masu Sulke Don Yaƙar ‘Yan Bindiga

Published

on

Gwamna Dikko Radda ya kaddamar da motoci masu sulke 10 domin yaki da ’yan bindiga da sauran masu tada kayar baya a Jihar Katsina.

Kamfanin Dillancin aLabarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito a yayin kaddamar da motocin ranar Litinin, Dikko Radda ya ce, za a raba motocin ne ga jami’an tsaron hadin gwiwa a jihar domin yakar ’yan bindiga da sauran masu aikata miyagun laifuka.

Ya bayyana cewa, za a kai motocin ne kananan hukumomi takwas da ’yan bindiga suka hana su sakat.

Kananan hukumomin sun hada da Safana da Batsari da Danmusa da Kankara.

Sai kuma Faskari, Sabuwa da Dandume da Jibia.

Ya ce, “Gwamnati ta kuduri aniyar kawar da ’yan bindiga da masu aikata miyagun laifuka a jihar Katsina.”

Radda ya kara da cewa, an samu nasarori da dama tun bayan fara aikin rundunar tsaro ta hadin gwiwa a jihar.

Ya kuma yabawa jami’an tsaro bisa kokarin da suke yi, inda ya bayar da tabbacin gwamnati za ta ci gaba da ba su tallafin da ya dace domin dawo da zaman lafiya a fadin jihar.

Gwamnan ya bukaci jama’ar jihar su rika taimaka wa jami’an tsaro da sahihan bayanai dangane da masu aikata miyagun laifuka a yankunansu a kan kari.

A nasa jawabin, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Dokta Nasiru Muazu-Danmusa, ya ce samar da motoci masu sulke ya nuna aniyar gwamnati na kare jama’a.

Ya ce, gwamnati za ta ci gaba da hada kai da jami’an tsaro domin kare al’umma da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

A nasa jawabin,  mataimakin kwamishinan ’yan sanda Ibrahim Saad, ya yaba wa gwamnati bisa samar da motocin, ya kuma yi alkawarin cewa za a raba su yadda ya kamata domin murkushe ’yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifuka

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara