Connect with us

Labarai

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Published

on

Daga Sani Dutsinma

Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah daga Gidauniyar NASARA a Jihar Kebbi.

Babbar Sakatariyar Yaɗa Labarai ta Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Khadijat Saidu ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta rabawa manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

Sanarwar ta ce an bada tallafin ne domin sanya farin ciki a zukatan marayu da zawarawa 1,000 a garin Kangiwa, a watan Ramadan da kuma bukukuwan Sallah.

Ta ƙara da cewa, Gidauniyar NASARA wadda Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris ta kafa, ta raba kayan Sallah ga marayu, yayin da aka bai wa zawarawa buhunan shinkafa domin su sami damar yin bukin Sallah cikin farin ciki tare da iyalansu.

Tawagar gidauniyar ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abdulrasheed Bala, wanda shi ne jami’in da ke kula da Gidauniyar a matakin jiha, ta isar da saƙon Uwargidan Gwamnan, inda ta jaddada muhimmancin kyautatawa da nuna karamci, musamman a wannan lokaci na watan Ramadan.

A cewarsa, wannan kyakkyawan shiri na daga cikin ƙoƙarin Hajiya Zainab na tabbatar da cewa kowa yana cikin annashuwa a wannan lokaci na ibada. Ya ƙara da cewa ayyukan alherin da gidauniyar ke yi suna da matuƙar tasiri a rayuwar marasa galihu.

Wasu daga cikin waɗanda suka amfana da tallafin sun bayyana farin cikinsu tare da gode wa Allah Madaukakin Sarki, sannan suka nuna matuƙar godiya ga wadda ta kafa gidauniyar, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris, da kuma tawagar Gidauniyar NASARA bisa wannan karamci da kulawa da suka nuna.

Labarai

Labarai13 hours ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai16 hours ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai20 hours ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai22 hours ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai1 day ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai1 day ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai1 day ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai1 day ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai4 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai4 days ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Mafi Shahara