Connect with us

Labarai

Gidauniyata Za Ta Ci Gaba Da Tallafawa Matasan Jihar Sakkwato – Seyi Tinubu

Published

on

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Samar da Dokar Shirye-Shiryen Matasa Da Ayyukan

 

Ministan ci gaban matasa, Ayodele Olawande, ya jaddada kudirin gwamnatin tarayya na karfafa matasa domin samar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin kasar nan.

 

Ministan ya ce ziyarar da ya kai jihar Sokoto na da nufin kara cudanya da matasa a cikin watan Ramadan da bayar da tallafi mai mahimmanci.

 

Olawande, wanda ya samu rakiyar Seyi Tinubu, ya jaddada mahimmancin shirye-shiryen da suka shafi matasa, ciki har da samar da dandalin tattaunawa kan ci gaban matasa na kasa.

 

Ya yi nuni da cewa, shugaban kasa Bola Tinubu da Gwamna Ahmed Aliyu suna da manufa daya na ci gaban matasa, ta yadda za a yi amfani da albarkatun da aka ware wa Sokoto yadda ya kamata.

 

Ministan ya kuma yaba da bullo da shirin ba da lamuni na dalibai, inda ya bayyana shi a matsayin wani gagarumin shiri na tallafawa daliban Najeriya.

 

Ya kuma ba da tabbacin cewa, akwai wasu shirye-shiryen da suka shafi matasa, inda Sokoto za ta ci gajiyar muhimman tsare-tsare a fannin noma, gidaje, da kuma shirye-shiryen horarwa.

 

Ya kuma kara ba da tabbacin cewa FG na kokarin samar da yanayi mai dacewa da matasan Najeriya za su ci gaba.

 

A nasa jawabin, gwamna Ahmed Aliyu na sokoto, ya bayyana ziyarar a matsayin wata shaida ga jajircewar da gwamnatin ta yi wajen karfafa matasa.

 

Ya yabawa Seyi Tinubu, wanda shine wanda ya assasa Renewed Hope Youth Empowerment Initiative, bisa gudunmawar da yake bayarwa a harkokin siyasa da ci gaban tattalin arziki, yana mai kira gare shi da ya mika shirye-shiryensa ga matasan Sokoto.

 

Gwamnan ya kuma bayyana irin kokarin da gwamnatin sa ke yi na tallafa wa matasa da suka hada da nada matasa a manyan mukamai a gwamnati da samar da ilimi kyauta ga dukkan dalibai ba tare da la’akari da addini ko kabila ba.

 

Ya yabawa Tinubu kan irin ayyukan alheri da yake yi a cikin watan Ramadan, musamman ga marasa galihu.

 

Tun da farko, Seyi Tinubu ya bayyana kudirinsa na ci gaban matasa a Sakkwato, inda ya yi alkawarin cewa gidauniyarsa za ta ci gaba da tallafa wa ayyuka a fadin kananan hukumomin jihar 23.

 

Nasir Malali

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara