Labarai
Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima
Fadar shugaban kasa ta musanta rahotannin da ke nuni da cewa an hana mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, GCON shiga fadar shugaban kasa, inda ta bayyana ikirarin a matsayin shirme, kage da kuma karya gaba daya.
Wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da sadarwa na ofishin mataimakin shugaban kasa Stanley Nkwocha ya sanyawa hannu, ta ce rahoton da wasu shafukan da ba su da tushe suka yada shi, na cikin jerin labaran karya da aka kitsa domin haifar da rashin jituwa tsakanin shugaban kasa da mataimakinsa.
Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan wani yunkuri ne mai rauni na cin mutuncin mutum da ofishin Mai Girma, Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima.
Nkwocha ya ce labarin da ake cewa sojoji dauke da makamai sun hana mataimakin shugaban kasa shiga fadar Shugaban kasa wato Villa ba wai kawai an yi ne ba haka kawai, a’a har ma ya nuna rashin fahimtar ayyukan gwamnati.
Sanarwar ta ce, wannan shi ne mafi girman furuci na fatar baka, kuma hakan yana nuni da cewa masu yin wannan tatsuniyoyi sun gaji da zargi da kuma hasashe, in ji sanarwar.
Wannan dai ba shi ne karon farko da fadar shugaban kasar ke yin watsi da irin wadannan rahotannin ba. Kwanaki kadan kafin hakan, ta karyata labaran karya da ke yawo a shafukan yakin neman zabe dauke da hoton shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu. Fadar shugaban kasar ta yi imanin cewa irin wannan karyar wani yunkuri ne na kawo cikas ga hadin kai da amincin shugabancin kasar.
Mataimakin shugaban kasar ya ci gaba da maida hankali kan ayyukan sa da kuma marawa shugaban kasar baya wajen cimma muradun ‘yan Najeriya. Sanarwar ta kara da cewa, ba shi da wani abin da zai raba hankali.
Nkwocha ya yabawa ‘yan Najeriya da ke ci gaba da nuna goyon bayansu ga gwamnatin Tinubu-Shettima, ya kuma bukaci kafafen yada labarai da su nemi bayanai daga majiyoyi masu inganci tare da yin taka-tsan-tsan wajen bayar da rahotanni masu ban sha’awa.
Sanarwar ta kara da cewa, “alkwarin da ke tsakanin wannan gwamnati da ‘yan Najeriya ya yiwu ne ta hanyar halaltaccen tsarin mulki.
Bello Wakili
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
