Connect with us

Kasuwanci

Dikko Radda Ya Kafa Dokar Haramta Ɓoye Kayan Abinci A Katsina

Published

on

Gwamnan Jihar Katsina Dikko Umaru Radda ya sa hannu kan dokar da za ta haramta wa ’yan kasuwa da kamfanoni boye kayan abinci.

Gwamnan ya kuma kafa wani kwamiti na musamman da zai bi lungu da sako na jihar domin zakulo mutanen da ke boye kayan abinci a sassan jihar.

Har wa yau, an kayyade nau’ikan kayan abinci da dokar za ta yi aiki a kansu da suka hada shinkafa, masara, gero, dawa, waken suya, gyada da duk wani nau’in kayan abinci da karancinsa zai jefa Katsinawa cikin halin ha’ula’i.

Dokar ta fayyace karara cewa duk wani mutum ko kamfani da aka samu da laifin boye kayan masarufi, za a iya hukunta shi karkashin sashe na 114 a kundin manyan laifuka na final kod.

Haka kuma, duk wani wurin da aka kama ana boye nau’ikan kayan abincin da dokar ta kayyade, za a bude shi sannan a fitar da kayan abincin domin sayar wa al’umma a farashin da ya dace.

Kwamitin na kar-ta-kwana mai mambobi 27 da Gwamna Radda ya kafa ya umarci jami’an tsaro da su kamo tare da gurfanar da duk wadanda aka samu da laifin yi wa sabuwar dokar karan-tsaye.

kwamitin zai gana da masu ruwa da tsaki kan harkar kayan masarufi a jihar, inda zai rika kula da yadda ake safarar kayan abincin daga sassan jihar daban-daban da ma tsallakawa da shi da ake yi a kasashen waje.

Mambobin kwamitin sun hada da Shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnatin Katsina, Alhaji Jabiru Salisu Abdullahi Tsari a matsayin jagora, sai Kwamishinoni a Ma’aikatar Shari’a da Yada Labarai da wakilan Sarakunan Katsina da Daura da wakilan kungiyoyin addini da ke jihar da sauransu.

Labarai

Labarai18 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi18 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai19 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai20 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara