Labarai
Majalisar Kaduna Ta Amince da Dokar Kafa Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arzikin na Zamani
Daga Shamsuddeen Mannir Atiku
Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da dokar kafa Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arzikin na Zamani ta Jihar Kaduna, wacce za ta taimaka wajen ƙarfafa tsarin fasaha na jihar da inganta gasa a fannin tattalin arziki.
Dokar mai taken “Kaduna State Information Technology and Digital Economy Agency and for Related Matters, 2025” ta samu amincewa bayan karatu na uku a zaman majalisar na ranar Talata.
Shugaban majalisar, Hon. Yusuf Dahiru Liman, wanda ya jagoranci zaman, ya bayyana muhimmancin dokar, yana mai cewa kafa hukumar zai faɗaɗa damar tattalin arziki tare da bai wa jihar Kaduna damar cin moriyar cigaban fasahar zamani a duniya.
Ya ce hukumar za ta ƙarfafa kirkire-kirkire, bunƙasa ƙwarewar dijital, da daidaita jihar da sauye-sauyen fasaha da tattalin arzikin dijital a duniya.

Tun da farko, shugaban kwamitin haɗin gwiwa kan Yada Labarai, Kungiyoyi Masu Zaman Kansu da Abokan Cigaba, Mr. Henry Marah Zakariah, ya gabatar da rahoton kwamitin.
Ya bayyana cewa an yi nazari mai zurfi kan dokar, kuma an tabbatar da cewa mataki ne mai muhimmanci wajen ƙara damar samun ayyukan yi da sauƙaƙa wa al’umma samun ilimin fasahar zamani.
Mr. Henry Zakariah ya kuma jaddada cewa kafa hukumar za ta bunƙasa tattalin arzikin jihar da samar da kudaden shiga, inda ya bayyana cewa za a kafa cibiyoyin fasahar zamanin a yankunan karkara domin bai wa kowa damar cin gajiyar ayyukan Hukumar.
Daga karshe majalisar ta amince da dokar baki ɗaya, bayan Dan Majalisa mai wakiltar mazabar Birnin Zaria, Barr. Mahmood Lawal Sama’ila ya gabatar da kudirin amincewa inda ya samu goyon baya daga Dan Majalisa mai wakiltar mazabar Makarfi, Isiyaku Ibrahim ya goyi bayan shi.
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
