Connect with us

Kasuwanci

Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?

Published

on

Yanzu ƴan Najeriya za su iya cire naira 100,000 ta na’urar cire kuɗi ta ATM a rana, haka ma abin yake a ɓangaren cire kuɗi ta na’urar POS.

A ɓangaren ma’aikatu kuma, za su iya cire kuɗi har naira miliyan biyar ne a duk mako.

Wannan na ƙunshe ne a cikin sabbin tsare-tsaren da Babban Bankin Najeriya CBN ya fitar bayan garambawul da ya yi kan dokokin cire kuɗi ta na’urar ATM da POS a Najeriya.

Bankin ya ce wannan sabuwar dokar za ta fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2026.

A cikin wata sanarwa da daraktan tsare-tsare na bankin, Dr Rita Sike ta fitar a ranar Talata 2 ga watan Disamba, ta ce babban bankin ya yi gyara ne a kan dokokin kuɗin da za a iya cirewa.

Amma idan mutum ya cire kuɗi sama da ƙa’idar da aka ƙayyade a mako, mutum zai biya wani adadi na kuɗin.

Ya kamata ƴan Najeriya su fahimci cewa ida suka shiga cikin banki suka cire naira 100,000, shi ma yana cikin kuɗin da suka cire a rana.

Hakan na nufin za a ƙirga shi a cikin kuɗin da mutum ya cire a makon, kamar ya cire ta ATM ko POS.

Me ya sa aka yi canjin?

Kamar yadda sanarwar ta nuna, an tsara tsohuwar dokar ce domin rage ta’ammali da tsabar kuɗi da magance matsalolin tsaro da ma daƙile sama da faɗi da kuɗaɗe da sauran abubuwan da ake tunanin ba su da sauƙi sai da tsabar kuɗi.

Sauran dokokin sun haɗa da:

Cire kuɗi mai yawa – Idan ka cire kuɗi sama da adadin da ƙayyade, za ka biya kashi uku, idan kuma ma’aikata ce za ta biya kashi biyar na kuɗin.

Amfani da takardar karɓar kuɗi a banki – Idan ka tura wani da takardar karɓar kuɗi wato ‘check’, shi ma za a ƙirga a cikin adadin kuɗin da ka cire a mako.

Yadda aka fara dokar

A watan Disamban 2022 ne babban bankin Najeriya ya sanar da cewa daga ranar 9 ga wata Janairun 2023, ɗaiɗaikun mutane ba za su cire kuɗi sama da naira 100,000 ba, ma’aikatu kuma naira 500,000.

Sannan a lokacin bankin ya ce adadin kuɗin da za a iya cirewa ta na’urar POS shi ne naira 20,000.

Haka kuma a lokacin bankin ya ƙayyade cewa ƙananan takardun kuɗi irin su naira 200 zuwa ƙasa ne za a riƙa sakawa a ATM.

Bankin ya fitar da tsare-tsaren ne bayan fitar da sababbin takardun kuɗi a Najeriya.

Idan mutum zai cire sama da adadin, zai biya kashi biyar, ma’aikatu kuma za su biya kashi 10.

A baya, kuɗin da mutum zai iya cirewa ta na’urar ATM naira 100,00 ne a mako, amma mutum naira 20,000 kawai zai iya cira a kullum, amma a POS kuma, naira 20,000 kawai za a iya cirewa.

Labarai

Labarai2 hours ago

NHIA Ta Fara Daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa a Jigawa

Usman Muhammad Zaria  Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa (NHIA) ta fara aikin daukar Jami’an Kula da Lafiya na...

Labarai7 days ago

Baragurbi a Aikin Jarida na Barazana ga Sahihancin Kafafen Yada Labarai – Shugaban NUJ-FRCN

Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen FRCN Kaduna, Kwamared Umar Adamu Sarkinfada, ya bayyana cewa mummunan aikin jarida...

Labarai2 weeks ago

Ƙaruwa a Shan Abubuwan Sha Masu Ƙara Ƙarfi na Haddasa Damuwar Lafiya a Kano

Abubuwan sha masu ƙara ƙarfi, waɗanda aka fi sani da energy drinks ko energizers, na ƙara samun karɓuwa a faɗin...

Labarai2 weeks ago

Shugaba Tinubu Ya Taya CPSO Usman Shugaba Murnar Cika Shekara 45 da Haihuwa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Kwamishinan ‘Yan Sanda, Usman Musa Shugaba, wanda shi ne Babban Jami’in Tsaron ‘Yan...

Labarai2 weeks ago

TSARO: Gwamnan Jihar Neja Ya Nuna Alhini Kan Harin ‘Yan Ta’adda a Al’ummomin Borgu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa kan harin ‘yan ta’adda da aka kai wa wasu...

Labarai2 weeks ago

Allah Ya Jikan Jarman Kauru Da Ke Jihar Kaduna

Mun sami labarin rasuwar tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Malam Suleiman Lawal Jarman Kauru. Malam Suleiman Lawal, mai shekaru...

Labarai2 weeks ago

Gwamnatin Kano Ta Faɗaɗa Damar Tattalin Arziki ga Mata da Masu Buƙata Ta Musamman

An kammala kasuwar baje kolin mata ta tsawon kwanaki huɗu, wadda Ma’aikatar Harkokin Mata, Yara da Masu Buƙata Ta Musamman...

Labarai2 weeks ago

Rundunar Tsaro Ta Haɗin Gwiwa Ta Hallaka ’Yan Bindiga 150

Rundunar tsaro ta haɗin gwiwa da ta ƙunshi Sojojin Nijeriya, Hukumar Tsaron Farin Ciki (DSS), ’Yan Sanda da sauran hukumomin...

Ilimi2 weeks ago

Gwamnatin Neja Ta Amince da Sake Buɗe Makarantun Gwamnati da Masu Zaman Kansu daga 12 ga Janairu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya amince da sake buɗe dukkan makarantun gwamnati da masu zaman kansu a faɗin...

Ilimi2 weeks ago

Gwamnatin Nasarawa Ta Roki Malaman Jami’o’i Masu Yajin Aiki Su Koma Aji – SSA Ahemba

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta yi kira ga malaman manyan makarantu mallakar jihar da ke yajin aiki da su janye yajin...

Mafi Shahara