Connect with us

Labarai

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

Published

on

 

By Adamu Yusuf

 

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki da ke kula da harkokin bala’o’i a Jihar Kaduna, sun sake haɗa karfi da karfe domin rage aukuwar bala’o’i a wannan shekarar.

 

Da yake magana a wajen taron masu ruwa da tsaki da ya gudana a ofishin NEMA da ke Kaduna domin duba abubuwan da suka faru na bala’o’i a shekarar da ta gabata, Shugaban Ayyuka na hukumar NEMA mai kula da jihohin Katsina da Kaduna, Suleiman Mohammed, ya ce hukumar ta sauya tsarin aikin ta daga bayar da taimako gaggawa bayan bala’i ya faru zuwa ɗaukar matakan kare faruwar bala’i baki daya.

 

Ya bayyana cewa bayan hukumomin da suka dace kamar Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya sun fitar da hasashen yanayi na kakar daminan bana, hukumar NEMA ta shirya irin wannan taron masu ruwa da tsaki tun farkon shekarar domin nazarin yiwuwar illolin da ka iya tasowa tare da tsara hanyoyin da za a bi wajen shawo kan bala’o’i.

 

A cewarsa, taron ya haɗa manyan masu ruwa da tsaki da suka tattauna hanyoyin da za su yi aiki tare wajen tunkarar bala’o’i tun kafin su faru da lokacin da suke faruwa, da kuma bayan sun faru.

 

Suleiman Mohammed ya kuma bayyana cewa haɗin gwiwar hukumomi kamar Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jiha (SEMA), Kungiyar Red Cross, Hukumar Kashe Gobara, Civil Defence da sauran hukumomi ya taimaka wajen magance wasu bala’o’i da suka faru a jihar a shekarar da ta gabata, ciki har da ambaliya, gobara da kuma hatsarin tankokin mai.

 

Ya tuna cewa an gudanar da wani atisayen kwaikwayo kan yadda za a magance hatsarin tankokin mai a Maraban Jos, domin nuna yanda hukumar take gudanar da ayyukan ceto da agajin gaggawa.

 

Ya ce, “Atisayen wanda ya haɗa da direbobin tankokin mai da sauran masu ruwa da tsaki, an shirya shi ne domin ƙarfafa shirin ko-ta-kwana da kuma tabbatar da haɗin gwiwar da ya dace idan irin waɗannan bala’o’i suka faru.”

 

Ya ƙara da cewa duk da cewa an samu wasu ambaliyar ruwa a yankuna kamar Kaduna North, Kaduna South, Zaria da kuma ƙaramar hukumar Sanga, saurin ɗaukar mataki da hukumomin agaji suka yi ya taimaka wajen rage illolin da bala’in ya jawo ga al’ummomin da abin ya shafa.

 

Shi ma da yake nasa jawabin, Shugaban Sashen Kula da Bala’o’i na Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Najeriya (NSCDC) a Jihar Kaduna, Mataimakin Kwamandan Hukumar Akaine King Michael, ya bayyana taron a matsayin mai muhimmanci kuma da ya zo a kan lokaci domin nazarin ayyukan kula da bala’o’i na shekarar da ta gabata.

 

Ya ce taron ya ba masu ruwa da tsaki damar tantance abubuwan da suka faru a shekarar 2025, musamman hatsarin tankokin mai da ke ɗauke da man fetur, wanda sau da dama kan haddasa zubar mai a kan hanyoyi tare da jefa rayuka da dukiyoyi cikin haɗari.

Michael ya kuma bayyana cewa hukumar NSCDC na ci gaba da aiki tare da NEMA wajen gudanar da ayyukan ceto yayin bala’o’i, inda ya ce babban aikin su shi ne fitar da mutanen da abin ya shafa daga wuraren haɗari, kulle wuraren da lamarin ya faru da kuma hana jama’a ɗiban mai idan tankar mai ta yi hatsari..

 

A nata jawabin, Shugabar Sashen Muhalli da Sauyin Yanayi da Makamashi na Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) a Jihar Kaduna, Rahmatu Suleiman, ta bayyana muhimmiyar rawar da hukumar ke takawa wajen wayar da kan jama’a da kuma haɗa kai da al’umma domin hana aukuwar bala’o’i.

 

Ta ce NOA na aiki kafada da kafada da NEMA wajen isar da saƙonnin wayar da kai ga al’ummomi a faɗin jihar, inda ta bayyana cewa hukumar na da ma’aikata a dukkan ƙananan hukumomi 23 na Jihar Kaduna da ke gudanar da wayar da kan jama’a kan haɗarin bala’o’i kamar ambaliya.

Rahmatu Suleiman ta ƙara da cewa hukumar na kuma aiki tare da kafafen yaɗa labarai domin ƙara wayar da kan jama’a, inda ta bayyana cewa Daraktan NOA na Jihar Kaduna, Danjuma Makama, kan bayyana a kafafen yaɗa labarai sau da dama domin ilmantar da jama’a kan matakan kariya da kuma hanyoyin rage illolin ambaliya da sauran bala’o’i.

 

Mahalartar taron sun jaddada muhimmancin ci gaba da haɗin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati, shugabannin al’umma da kuma jama’a domin hana aukuwar bala’o’i da kuma tabbatar da saurin kai dauki idan suka faru.

 

Sun kuma yi kira a ci gaba da gudanar da shirye-shiryen wayar da kan jama’a domin gujewa halayen da kan jawo hatsari ko ƙara tsananta matsaloli, musamman a lokutan hatsarin tankokin mai da kuma ambaliya.

Labarai

Labarai3 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai1 day ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi1 day ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara