Labarai
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki Da Dama A Karamar Hukumar Bodinga
Daruruwan iyalai da manoma sun shiga cikin muwuyacin hali sakamakon iftila’in ambaliya da ta afka a kauyen Badau da ke gundumar Darhela da Butuku a gundumar Toma, ƙaramar hukumar Bodinga a jihar Sakkwato.
Ambaliyar ta nutse da dubban gonaki, ta rusa gidaje, tare da lalata kasuwar garin Dandin-Mahe da ke cikin ƙaramar hukumar Shagari, abin da ya jefa al’ummar yankin cikin tashin hankali.

A cewar rahoton farko, sama da gonaki 3,000 ne suka lalace a Badau, yayin da gonaki 75 suka lalace a Butuku.
Bisa ga rahoton hukumar ƙaramar hukumar Bodinga, tawagar haɗin gwiwa daga Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Sakkwato (SEMA) da Hukumar Kula da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), ofishin Sakkwato, sun kai ziyara yankunan da lamarin ya shafa domin tantance irin asarar da aka yi.

Jagoran tawagar shi ne Daraktan Tallafi da Sake Gina Rayuwa na SEMA, Malam Mustapha Umar, tare da jami’in tsare-tsare na NEMA a Sakkwato, Mista Tukur Abubakar.
Rediyon Najeriya a Sakkwato ya ruwaito cewa iftila’in ya biyo bayan ruwan sama mai ƙarfi da aka kwashe kwanaki huɗu ana yi lokaci zuwa lokaci a yankin.

Mazauna yankin sun roƙi gwamnatin jiha da ta tarayya da su kawo tallafin gaggawa domin rage musu ƙuncin da suke ciki.
Tawagar SEMA da NEMA sun tabbatar wa mazauna yankin cewa za su tattara bayanan da suka tara domin gabatar wa ga hukumomi don hanzarta kawo agajin gaggawa.

Tawagar ta kuma kai ziyara wasu yankuna a cikin ƙaramar hukumar Shagari inda ambaliyar ta shafi ƙauyuka huɗu, tare da lalata kasuwa da gonaki 74, da kuma jawo asarar gine-gine.
Har ila yau, wani gida ya rushe sakamakon ambaliyar, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar yaro mai shekaru bakwai mai suna Jafar Sani.
Daga Nasiru Malali
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
