Connect with us

Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki Da Dama A Karamar Hukumar Bodinga

Published

on

Daruruwan iyalai da manoma sun shiga cikin muwuyacin hali  sakamakon iftila’in ambaliya da ta afka a kauyen Badau da ke gundumar Darhela da Butuku a gundumar Toma, ƙaramar hukumar Bodinga a jihar Sakkwato.

Ambaliyar ta nutse da dubban gonaki, ta rusa gidaje, tare da lalata kasuwar garin Dandin-Mahe da ke cikin ƙaramar hukumar Shagari, abin da ya jefa al’ummar yankin cikin tashin hankali.

A cewar rahoton farko, sama da gonaki 3,000 ne suka lalace a Badau, yayin da gonaki 75 suka lalace a Butuku.

Bisa ga rahoton hukumar ƙaramar hukumar Bodinga, tawagar haɗin gwiwa daga Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Sakkwato (SEMA) da Hukumar Kula da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), ofishin Sakkwato, sun kai ziyara yankunan da lamarin ya shafa domin tantance irin asarar da aka yi.

Jagoran tawagar shi ne Daraktan Tallafi da Sake Gina Rayuwa na SEMA, Malam Mustapha Umar, tare da jami’in tsare-tsare na NEMA a Sakkwato, Mista Tukur Abubakar.

Rediyon Najeriya a Sakkwato ya ruwaito cewa iftila’in ya biyo bayan ruwan sama mai ƙarfi da aka kwashe kwanaki huɗu ana yi lokaci zuwa lokaci a yankin.

Mazauna yankin sun roƙi gwamnatin jiha da ta tarayya da su kawo tallafin gaggawa domin rage musu ƙuncin da suke ciki.

Tawagar SEMA da NEMA sun tabbatar wa mazauna yankin cewa za su tattara bayanan da suka tara domin gabatar wa ga hukumomi don hanzarta kawo agajin gaggawa.

Tawagar ta kuma kai ziyara wasu yankuna a cikin ƙaramar hukumar Shagari inda ambaliyar ta shafi ƙauyuka huɗu, tare da lalata kasuwa da gonaki 74, da kuma jawo asarar gine-gine.

Har ila yau, wani gida ya rushe sakamakon ambaliyar, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar yaro mai shekaru bakwai mai suna Jafar Sani.

 

Daga Nasiru Malali

 

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci7 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara