Kasuwanci
Gwamnatin Sakkwato Ta Kashe Naira Miliyan 60 Kan Koyon Sana’o’i
Gwamnatin Jihar Sakkwato ta kaddamar da rabon kuɗaɗe har Naira miliyan sittin ga matasa dari shida da aka horas a sana’o’i daban-daban a ƙarƙashin shirin koyon sana’o’i na jihar.
A yayin bikin miƙa takardun cekin kudin ga waɗanda suka ci gajiyar shirin, gwamnan jihar, wanda Mai Ba Shi Shawara na Musamman kan Cigaban Al’umma, Alhaji Garba Maitumbi Kebbe ya wakilta, ya bayyana cewa shirin horaswar an tsara shi ne domin ƙarfafa matasa su dogara da kansu tare da ba da gudummawa wajen bunƙasa ci gaban jihar.
Ahmad Aliyu ya ce gwamnatinsa na da cikakken ƙuduri na tallafa wa bunƙasar ƙananan da matsakaitan masana’antu, a matsayin muhimmin ginshiƙi na bunƙasar tattalin arzikin jihar.
A nata jawabin, Babbar Sakatariyar Hukumar Bunƙasa Ƙananan da Matsakaitan Masana’antu ta Jihar Sakkwato (SOSMEDA), Hajiya Binta Usman, ta ce waɗanda suka amfana da shirin—waɗanda SOSMEDA tare da Sashen Cigaban Al’umma suka horas—sun karɓi Naira dubu ɗari-ɗari kowannensu tare da kayan aikin sana’a domin tallafa musu wajen fara kasuwanci.
Ta ƙara da cewa hukumar ta riga ta horas da matasa sama da dubu uku da ɗari bakwai da hamsin a faɗin jihar.
NASIR MALALI
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
