Connect with us

Kasuwanci

An Bukaci Mazauna Rukunin Gidaje Harmony Su Rika Biyan Bashin Gidajensu

Published

on

An bukaci mazauna Rukunin gidajen Harmony da ke jihar Kwara da su ƙara ƙaimi wajen biyan bashin lamunin gidajensu (mortgage), domin bai wa wasu ma damar cin gajiyar shirin mallakar gidaje.

Manajan reshen Bankin Lamunin Gidaje na Tarayya (Federal Mortgage Bank of Nigeria – FMBN) na jihar Kwara, Alhaji Nurudeen Aliyu Muhammed, ne ya yi wannan kira a yayin bikin rantsar da mambobin kwamitin mazauna Harmony Estate da aka gudanar a Ilorin.

Ya bayyana cewa yawancin mazauna gidan ba su cika ka’idojin mallakar gidajen ba saboda rashin cika sharuddan biyan bashin.

A cewarsa, bankin ya yi haƙuri tsawon lokaci tare da barin masu zama a gidajen ba tare da biyan kuɗaɗen da suka dace ba.

Alhaji Nurudeen ya gargadi mazauna da su yi abin da ya dace domin kauce wa korar su daga gidajen.

Ya kuma bayyana cewa nan ba da jimawa ba bankin zai fara gina wani sabon rukuni na gidaje da za a sayar da kowanne a kan kuɗi Naira miliyan 25.

Manajan ya ƙara da cewa za a samar da sabbin matakan tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron lafiyar al’ummar yankin.

A nasa jawabin yayin bikin rantsar da kwamitin, Shugaban Mazauna Harmony Estate Ilorin, Malam Otepola Adeolu, ya shawarci mambobin kwamitin da su kasance masu halartar tarurrukansu cikin lokaci.

Ya ce manufar kafa kwamitin ita ce bai wa mambobin damar samun sahihin bayani kai tsaye kan al’amuran da suka shafi mazauna gidan.

Malam Adeolu ya kuma shawarci mazauna yankin da su tabbatar suna biyan kuɗaɗen wata-wata da na wutar lantarki da ruwa yadda ya kamata.

Haka zalika, ya bukaci mambobin kwamitin da su rika adana bayanan ayyuka da kuma cikakkun bayanai na dukkan mazauna gidaje kusan 500 da ke cikin estate ɗin.

Shugaban ya yi kira ga hadin kan dukkan mambobi domin tabbatar da nasarar aiwatar da ayyukansu a sabuwar shekara.

Ali Muhammad Rabiu

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara