Ilimi
Gwamnati Za Ta Ci Gaba Da Inganta Lafiya A Jihar Sakkwato
Gwamnatin jihar Sokoto ta ce za ta ci gaba da jajircewa wajen inganta fannin kiwon lafiya a jihar.
Mataimakin gwamnan jihar Alhaji Idris Mohamed Gobir ya bayyana cewa yayin da ya karbi bakuncin sabuwar wakiliyar Unicef ta kasa Mrs Wafaa Sa’eed da ta kai ziyarar fahimtar da jihar.
Alhaji Idris Gobir ya ce a kan haka ne bangaren ke samun mafi yawan kasafin kudi tun hawan gwamnatin mai ci.
A wata sanarwa da Daraktan hulda da manema labarai (Mataimakin Gwamnan) Garba Muhammed ya raba wa manema labarai, Mataimakin Gwamnan ya ce manufar ita ce a tabbatar da cewa mutane suna samun ayyukan kiwon lafiya cikin sauki.
Ya kuma nuna jin dadinsa da tallafin daban-daban da gwamnatin jihar ke samu daga Unicef domin inganta fannin lafiya.
Alhaji Idris Gobir ya bada tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da bayar da duk wani goyon bayan da Unicef ke bukata domin gudanar da ayyukansu cikin kwanciyar hankali a jihar.
Tun da farko, sabuwar wakiliyar kasar Misis Wafaa Sa’eed ta ce ayyukan Unicef sun shafi jin dadin mutane musamman yara a duniya.
Misis Wafaa Sa’eed ta sanar da cewa Unicef za ta taimaka wa yara marasa galihu 18,000 a shirin inshorar lafiya a jihar.
Ta ci gaba da cewa Asusun ya samar da wayoyin hannu guda 200 da kuma abin caji wato Power Bank da kuma Kwamfutar laptop 3 na rijistar zamantakewa a jihar.
Wakilin Unicef na kasa tare da rakiyar sabon mataimakin wakilin kasar mai kula da ayyuka Mista Charles Opikoli Lolika ya bayyana jin dadinsa tare da hadin gwiwar da asusun ke samu daga gwamnatin jihar tare da fatan za a dore.
REL/MUSTAPHA
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
