Ilimi
Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta
By Adamu Yusuf
Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan tsaftace bayanai da rubuta rahotanni da zai taimaka wajen rage karuwar yawan yara da basu zuwa makaranta a cikin al’ummomin makiyaya a kasar nan.
Babban Daraktan a Hukumar, Dr. Abdu Umar Hardo, ya bayyana hakan yayin bude taron da aka gudanar a hedkwatar hukumar dake Kaduna.
Dr. Umar Hardo ya ce horon yana karkashin hadin gwiwa ne tsakanin Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da Hukumar Ilimantar da Makiyaya ta kasa da Hukumar Ilimin da Al-Majirai da Hukumar Ilimintar da Jama’a (NCME) da dai sauransu.

Ya kara da cewa shirin yana nufin baiwa ma’aikata kwarewa wajen nazari da sarrafa bayanan da aka tattara da aka samo domin aiwatar da shirye-shiryen don rage yawan yaran makiyaya da basa zuwa makaranta.
Dr. Hardo ya ce hukumar an dora mata alhakin rage yawan yara da basu zuwa makaranta ba a cikin al’ummomin makiyaya kawai ba har da masu kamun kifi da manoma a fadin kasar.
A cewarsa, kimanin yara miliyan 5.5 daga al’ummomin makiyaya ba sa zuwa makaranta a yayin da kimanin yara miliyan 1.5 ke halartar makaranta, lamarin da ke nuna babban gibi da shirin ke nufin magancewa.
Ya kara da cewa kwanan nan hukumar ta gudanar da binciken taswira a jihohi shida da Babban Birnin Tarayya (FCT), ciki har da Jigawa, Gombe, Nasarawa, Enugu, Cross River, da Oyo, inda aka gano kimanin yara da matasa 660,000 da basu zuwa makaranta ba.
A jawabin sa, Professor Aminu Abdul Bichi, kwararre daga African Institute for Solution Development, ya ce horon ya mayar da hankali ne kan kididigar bayanai da aka samu wanda hakan zai taimaka wajen tsara yanda za’a dawo dasu makaranta.
Professor Bichi ya bayyana cewa nazarin bayanai ya nuna cewa kimanin kashi 62 cikin 100 na yara makiyaya ba su zuwa makaranta, yayin da kashi 32 cikin 100 suka daina zuwa makaranta a matakin firamare.
Ya kara da cewa 3.2 cikin 100 sun daina makaranta a matakin sakandare na farko, yayin da 1.2 cikin 100 suka daina a sakandare na gaba.
Professor Bichi ya ce wadannan bayanai sun nuna babbar matsalar kuma suna nuni da bukatar shirye-shirye na musamman da suka dogara da bayanai domin tabbatar da cewa yara daga al’ummomin makiyaya suna samun damar ilimi.
A ganawa da Radio Nigeria, Daraktar Tsare-Tsare, Bincike da Kididdiga a Hukumar, Dr. Rose Nkechi Nwaji, ta ce rungumar Shirin Ilimin Firamare Na musamman zai taimaka wajen rage yawan yara da basu zuwa makaranta musamman a cikin al’ummomin makiyaya.
Dr. Nwaji ta ce shirin, zai baiwa yara da suka daina zuwa makarantar damar karatu domin su shiga tsarin ilimi na kasa.

Ana sa ran mahalarta horon za su nazarci bayanan da aka tattara domin amfanin da su wajen tsara manufofi da za’a yi amfani dasu wajen maganin matsalar rashin zuwa makaranta na yaran makiyaya ta amfanin da sabon Shirin Ilimin Firamare na (ABEP).
-
Labarai6 days agoAna Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
-
Labarai7 days agoJam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano
-
Labarai5 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoGwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya
-
Labarai4 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai4 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
