Connect with us

Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi

Published

on

Gwamnatin Jihar Zamfara ta ayyana dokar ta-baci kan cutar shan-inna a Karamar Hukumar Gummi domin dakile yaduwar cutar da kuma kara karfafa ayyukan rigakafi.

 

Kwamishinar Lafiya ta jihar, Dakta Nafisa Muhammad Maradun, ta bayyana hakan a taron wata-wata na kwamitin kula da harkokin kiwon lafiya na matakin farko da aka gudanar a ofishin Mataimakin Gwamnan jihar a Gusau.

 

Ta ce matakin zai taimaka wajen kara sa ido kan cutar, fadada shirin allurar rigakafi da kuma wayar da kan al’umma domin hana yaduwar ta.

 

Mataimakin Gwamnan jihar, Mani Mallam Mummuni, ya jaddada muhimmancin allurar rigakafi wajen kare lafiyar jama’a musamman yara.

 

Ya kuma bayyana cewa a watan Maris za a gudanar da gangamin allurar rigakafin shan-inna wanda ake sa ran zai kai ga sama da yara miliyan daya da dubu dari uku a fadin jihar.

 

Haka kuma ya bukaci hukumomin lafiya su tabbatar da cewa alluran sun isa ga yaran da aka tsara su karba.

 

Shi ma mai kula da ayyukan Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) a jihar, Dakta Raji Mukhtar, ya tabbatar da cewa za su ci gaba da bai wa gwamnatin Zamfara goyon baya wajen kawo karshen cutar shan-inna.

Aminu Dalhatu/Gusau

Labarai

Labarai6 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai1 day ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi1 day ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara