Kasuwanci
An Bukaci Mazauna Rukunin Gidaje Harmony Su Rika Biyan Bashin Gidajensu
An bukaci mazauna Rukunin gidajen Harmony da ke jihar Kwara da su ƙara ƙaimi wajen biyan bashin lamunin gidajensu (mortgage), domin bai wa wasu ma damar cin gajiyar shirin mallakar gidaje.
Manajan reshen Bankin Lamunin Gidaje na Tarayya (Federal Mortgage Bank of Nigeria – FMBN) na jihar Kwara, Alhaji Nurudeen Aliyu Muhammed, ne ya yi wannan kira a yayin bikin rantsar da mambobin kwamitin mazauna Harmony Estate da aka gudanar a Ilorin.
Ya bayyana cewa yawancin mazauna gidan ba su cika ka’idojin mallakar gidajen ba saboda rashin cika sharuddan biyan bashin.
A cewarsa, bankin ya yi haƙuri tsawon lokaci tare da barin masu zama a gidajen ba tare da biyan kuɗaɗen da suka dace ba.
Alhaji Nurudeen ya gargadi mazauna da su yi abin da ya dace domin kauce wa korar su daga gidajen.
Ya kuma bayyana cewa nan ba da jimawa ba bankin zai fara gina wani sabon rukuni na gidaje da za a sayar da kowanne a kan kuɗi Naira miliyan 25.
Manajan ya ƙara da cewa za a samar da sabbin matakan tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron lafiyar al’ummar yankin.
A nasa jawabin yayin bikin rantsar da kwamitin, Shugaban Mazauna Harmony Estate Ilorin, Malam Otepola Adeolu, ya shawarci mambobin kwamitin da su kasance masu halartar tarurrukansu cikin lokaci.
Ya ce manufar kafa kwamitin ita ce bai wa mambobin damar samun sahihin bayani kai tsaye kan al’amuran da suka shafi mazauna gidan.
Malam Adeolu ya kuma shawarci mazauna yankin da su tabbatar suna biyan kuɗaɗen wata-wata da na wutar lantarki da ruwa yadda ya kamata.
Haka zalika, ya bukaci mambobin kwamitin da su rika adana bayanan ayyuka da kuma cikakkun bayanai na dukkan mazauna gidaje kusan 500 da ke cikin estate ɗin.
Shugaban ya yi kira ga hadin kan dukkan mambobi domin tabbatar da nasarar aiwatar da ayyukansu a sabuwar shekara.
Ali Muhammad Rabiu
-
Labarai7 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai7 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai4 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai7 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai4 days agoGwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya
-
Labarai4 days agoSojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina
-
Labarai6 days agoRamadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji
-
Labarai7 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
