Connect with us

Kasuwanci

An Bukaci Mazauna Rukunin Gidaje Harmony Su Rika Biyan Bashin Gidajensu

Published

on

An bukaci mazauna Rukunin gidajen Harmony da ke jihar Kwara da su ƙara ƙaimi wajen biyan bashin lamunin gidajensu (mortgage), domin bai wa wasu ma damar cin gajiyar shirin mallakar gidaje.

Manajan reshen Bankin Lamunin Gidaje na Tarayya (Federal Mortgage Bank of Nigeria – FMBN) na jihar Kwara, Alhaji Nurudeen Aliyu Muhammed, ne ya yi wannan kira a yayin bikin rantsar da mambobin kwamitin mazauna Harmony Estate da aka gudanar a Ilorin.

Ya bayyana cewa yawancin mazauna gidan ba su cika ka’idojin mallakar gidajen ba saboda rashin cika sharuddan biyan bashin.

A cewarsa, bankin ya yi haƙuri tsawon lokaci tare da barin masu zama a gidajen ba tare da biyan kuɗaɗen da suka dace ba.

Alhaji Nurudeen ya gargadi mazauna da su yi abin da ya dace domin kauce wa korar su daga gidajen.

Ya kuma bayyana cewa nan ba da jimawa ba bankin zai fara gina wani sabon rukuni na gidaje da za a sayar da kowanne a kan kuɗi Naira miliyan 25.

Manajan ya ƙara da cewa za a samar da sabbin matakan tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron lafiyar al’ummar yankin.

A nasa jawabin yayin bikin rantsar da kwamitin, Shugaban Mazauna Harmony Estate Ilorin, Malam Otepola Adeolu, ya shawarci mambobin kwamitin da su kasance masu halartar tarurrukansu cikin lokaci.

Ya ce manufar kafa kwamitin ita ce bai wa mambobin damar samun sahihin bayani kai tsaye kan al’amuran da suka shafi mazauna gidan.

Malam Adeolu ya kuma shawarci mazauna yankin da su tabbatar suna biyan kuɗaɗen wata-wata da na wutar lantarki da ruwa yadda ya kamata.

Haka zalika, ya bukaci mambobin kwamitin da su rika adana bayanan ayyuka da kuma cikakkun bayanai na dukkan mazauna gidaje kusan 500 da ke cikin estate ɗin.

Shugaban ya yi kira ga hadin kan dukkan mambobi domin tabbatar da nasarar aiwatar da ayyukansu a sabuwar shekara.

Ali Muhammad Rabiu

Labarai

Labarai53 minutes ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai1 hour ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai1 hour ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai1 hour ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai1 hour ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai2 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai2 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai3 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai4 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara