Labarai
Gwamnatin Jigawa ta Baiwa Kungiyar Tsoffin Sojoji Gagarumar Gudummawa
Daga Usman Muhammad Zaria
Kungiyar Tsoffin Sojoji reshen jihar Jigawa ta samu tallafin sama da naira miliyan 40 a wajen taron kaddamar da Gidauniyar Tallafawa Kungiyar na bana, wanda aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse.
Da yake jawabi a wajen taron, Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya bayyana matuƙar godiyarsa ga irin sadaukarwar da mambobin Legion suka yi, ciki har da waɗanda suka sadaukar da rayukansu wajen hidimtawa ƙasa.

Ya jaddada cewa irin wannan sadaukarwa za ta ci gaba da kasancewa a tarihin ƙasa, tare da tabbatar da cewa Gwamnatin Jihar Jigawa da al’ummar jihar za su ci gaba da nuna godiya da tallafa wa tsoffin sojojin domin samun ingantacciyar rayuwa.
Gwamna Namadi ya sanar da bayar da gudummawar Naira miliyan 10 daga gwamnatin jihar, tare da tasa gudummawar ta Naira miliyan 2. Mataimakin Gwamna, Injiniya Aminu Usman, shi ma ya bayar da Naira miliyan 2, yayin da ƙananan hukumomi 27 na jihar suka bayar da gudummawar haɗin gwiwa ta Naira miliyan 13.

Sauran manyan gudummawa sun haɗa da na mambobin Majalisar Zartarwa ta Jihar, Shugaban Ma’aikatan Gwamnati (Head of Service), Manyan Mataimaka da Masu Ba Gwamna Shawara na Musamman, shugabannin hukumomin tsaro, da kuma Kungiyar ‘Yan Jaridu ta Correspondents’ Chapel, wadda ta bayar da Naira dubu 100.
A jawabin, Shugaban Kungiyar Tsoffin Sojojin Nijeriya a Jihar Jigawa, Malam Aliyu Mustapha, ya gode wa gwamnatin jihar da al’ummar jihar baki ɗaya bisa ƙauna, tausayi da girmamawa da suke nuna wa mambobin Legion.

Ya bayyana cewa irin wannan kyakkyawar mu’amala tana ƙara ƙarfafa gwiwar kowa a cikin al’umma, tare da nuna cewa ba a manta da sadaukarwar da suka yi a baya ba.
“Ga ’yan uwana tsoffin sojoji, ina tabbatar muku da cewa Gwamnatin Jihar Jigawa na tsaye daram tare da mu,” in ji Shugaban.
“Ina matuƙar jin daɗin wannan karamci, kuma ina sake tabbatar da kudurin Kungiyar Tsoffin Sojojin Najeriya na ci gaba da fafutuka da hulɗa tare domin inganta walwalar dukkan mambobin Legion a faɗin jihar.”
-
Labarai3 days agoGwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah
-
Labarai6 days agoKwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara
-
Labarai6 days agoJami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi
-
Labarai6 days agoAn Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya
-
Labarai6 days agoMatashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba
-
Labarai2 days agoGidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days ago‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa
-
Labarai3 days agoJIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah
