Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa ta Baiwa Kungiyar Tsoffin Sojoji Gagarumar Gudummawa

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Kungiyar Tsoffin Sojoji reshen jihar Jigawa ta samu tallafin sama da naira miliyan 40 a wajen taron kaddamar da Gidauniyar Tallafawa Kungiyar na bana, wanda aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya bayyana matuƙar godiyarsa ga irin sadaukarwar da mambobin Legion suka yi, ciki har da waɗanda suka sadaukar da rayukansu wajen hidimtawa ƙasa.

Ya jaddada cewa irin wannan sadaukarwa za ta ci gaba da kasancewa a tarihin ƙasa, tare da tabbatar da cewa Gwamnatin Jihar Jigawa da al’ummar jihar za su ci gaba da nuna godiya da tallafa wa tsoffin sojojin domin samun ingantacciyar rayuwa.

Gwamna Namadi ya sanar da bayar da gudummawar Naira miliyan 10 daga gwamnatin jihar, tare da tasa gudummawar ta Naira miliyan 2. Mataimakin Gwamna, Injiniya Aminu Usman, shi ma ya bayar da Naira miliyan 2, yayin da ƙananan hukumomi 27 na jihar suka bayar da gudummawar haɗin gwiwa ta Naira miliyan 13.

Sauran manyan gudummawa sun haɗa da na mambobin Majalisar Zartarwa ta Jihar, Shugaban Ma’aikatan Gwamnati (Head of Service), Manyan Mataimaka da Masu Ba Gwamna Shawara na Musamman, shugabannin hukumomin tsaro, da kuma Kungiyar ‘Yan Jaridu ta Correspondents’ Chapel, wadda ta bayar da Naira dubu 100.

A  jawabin, Shugaban Kungiyar Tsoffin Sojojin Nijeriya a Jihar Jigawa, Malam Aliyu Mustapha, ya gode wa gwamnatin jihar da al’ummar jihar baki ɗaya bisa ƙauna, tausayi da girmamawa da suke nuna wa mambobin Legion.

Ya bayyana cewa irin wannan kyakkyawar mu’amala tana ƙara ƙarfafa gwiwar kowa a cikin al’umma, tare da nuna cewa ba a manta da sadaukarwar da suka yi a baya ba.

Ga ’yan uwana tsoffin sojoji, ina tabbatar muku da cewa Gwamnatin Jihar Jigawa na tsaye daram tare da mu,” in ji Shugaban.

Ina matuƙar jin daɗin wannan karamci, kuma ina sake tabbatar da kudurin Kungiyar Tsoffin Sojojin Najeriya na ci gaba da fafutuka da hulɗa tare domin inganta walwalar dukkan mambobin Legion a faɗin jihar.”

 

 

Labarai

Labarai7 hours ago

Sarkin Musulmi Ya Ayyana Ranar Juma’a 1 ga Watan Shawwal

Daga Nasir Malali Mai Martaba Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar, ya ayyana ranar Juma’a, 20 ga watan Maris a matsayin...

Labarai2 days ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai3 days ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai3 days ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai3 days ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai3 days ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai3 days ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai6 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Mafi Shahara