Connect with us

Labarai

Majalisar Kaduna Ta Amince da Dokar Kafa Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arzikin na Zamani

Published

on

Daga Shamsuddeen Mannir Atiku 

Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da dokar kafa Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arzikin na Zamani ta Jihar Kaduna, wacce za ta taimaka wajen ƙarfafa tsarin fasaha na jihar da inganta gasa a fannin tattalin arziki.

Dokar mai taken “Kaduna State Information Technology and Digital Economy Agency and for Related Matters, 2025” ta samu amincewa bayan karatu na uku a zaman majalisar na ranar Talata.

Shugaban majalisar, Hon. Yusuf Dahiru Liman, wanda ya jagoranci zaman, ya bayyana muhimmancin dokar, yana mai cewa kafa hukumar zai faɗaɗa damar tattalin arziki tare da bai wa jihar Kaduna damar cin moriyar cigaban fasahar zamani a duniya.

Ya ce hukumar za ta ƙarfafa kirkire-kirkire, bunƙasa ƙwarewar dijital, da daidaita jihar da sauye-sauyen fasaha da tattalin arzikin dijital a duniya.

Tun da farko, shugaban kwamitin haɗin gwiwa kan Yada Labarai, Kungiyoyi Masu Zaman Kansu da Abokan Cigaba, Mr. Henry Marah Zakariah, ya gabatar da rahoton kwamitin.

Ya bayyana cewa an yi nazari mai zurfi kan dokar, kuma an tabbatar da cewa mataki ne mai muhimmanci wajen ƙara damar samun ayyukan yi da sauƙaƙa wa al’umma samun ilimin fasahar zamani.

Mr. Henry Zakariah ya kuma jaddada cewa kafa hukumar za ta bunƙasa tattalin arzikin jihar da samar da kudaden shiga, inda ya bayyana cewa za a kafa cibiyoyin fasahar zamanin a yankunan karkara domin bai wa kowa damar cin gajiyar ayyukan Hukumar.

Daga karshe majalisar ta amince da dokar baki ɗaya, bayan Dan Majalisa mai wakiltar mazabar Birnin Zaria, Barr. Mahmood Lawal Sama’ila ya gabatar da kudirin amincewa inda ya samu goyon baya daga Dan Majalisa mai wakiltar mazabar Makarfi, Isiyaku Ibrahim ya goyi bayan shi.

 

Labarai

Labarai18 minutes ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai26 minutes ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai28 minutes ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai30 minutes ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai33 minutes ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai1 day ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai2 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai2 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai2 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai3 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara