Connect with us

Fasaha

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawa Na 2025

Published

on

Hukumar shirya jarabawar ta kasa NECO ta fitar da jarabawar SSCE dalibai dubu 818, 492 suka sami kiridit 5 zuwa sama da suka hada darasin Ingilishi da Lissafi.

 

Adadin bisa ga sakamakon ya nuna dalibai kashi sittin da biyu sun smai nasara.

 

Magatakardar NECO kuma Babban Jami’in Hukumar, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ne ya bayyana haka a lokacin da yake fitar da sakamakon jarabawar SSCE na shekarar 2025 a hedkwatar NECO da ke Minna babban birnin Jihar Neja.

 

Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ya bayyana cewa adadin dalibai miliyan daya da dubu dari da arba’in da hudu da dubu dari hudu da casa’in da shida da ke wakiltar maki tamanin da hudu da suka zana jarrabawar sun samu kiridit 5 ko sama da haka ba tare da la’akari da harshen Ingilishi da lissafi ba.

 

A cewar Farfesa Danteni “. A yayin gudanar da jarrabawar kammala sakandare ta shekarar 2025, (SSCE), an gano makarantu talatin da takwas suna yin magudin zabe) a jihohi talatin, yana mai jaddada cewa, za a gayyace su zuwa majalisar domin tattaunawa, bayan haka za a sanya takunkumin da ya dace.

 

Shugaban Hukumar NECO ya yi nuni da cewa an ba manya jami’ai Tara, Uku a Kogi, Daya a Niger, Uku a F.C.T, Daya a Kano da Daya a Jihohin Osun takardar gargadi saboda rashin kulawar da ake yi, wanda ya sa aka samu makara, rashin da’a, cin zarafi, da rashin biyayya.

 

Ya ce a lokacin Jarrabawar an samu rikicin kabilanci wanda ya haifar da bullar takardun jarrabawar a Jihar Adamawa daga ranar 7 zuwa 25 ga watan Yulin 2025 da ya shafi makarantu Takwas (8), inda ya ce jimillar darussa goma sha uku da takardu ashirin da tara (29) ne wannan lamarin ya shafa, sannan kuma dalibai dari biyar da casa’in da tara ne abin ya shafa.

 

NECO ta fara tattaunawa da jihar Adamawa da nufin gudanar da jarrabawar makarantun da abin ya shafa, inda ya nuna cewa ba za a iya fitar da sakamakon makarantun takwas a yanzu ba.” Inji magatakardan NECO.

 

Farfesa Dantani Wushishi ya bayyana cewa an fitar da sakamakon jarrabawar cikin gida na SSCE kwanaki hamsin da hudu bayan rubuta na karshe a watan Agusta, 2025, wanda ke nuni da cewa an kammala dukkan matakan da suka kai ga samun nasarar fitar da sakamakon cikin gida na 2025 SSCE.

 

Ya kara da cewa, fitar da sakamakon na cikin 2025 na SSCE cikin sauki, shaida ne na ma’aikatan Hukumar Jarrabawar bisa kwarewa, da’a da kuma ci gaba da neman nagartarsu, da sanin ya kamata, da kula da inganci, da jajircewa wajen bin ka’idojin da’a, sun tabbatar da cewa NECO ta samar da sakamakon da ya dace kuma dalibai, cibiyoyi da sauran jama’a suka amince da su.

 

 

Farfesa Dantani ya bayyana matukar godiya ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinuba bisa jajircewarsa wajen ganin an inganta ilimi ya samar da kyakkyawan yanayi ga hukumar NECO ta samu ci gaba, ya kuma yabawa ministan ilimi Dr Maruf Tunji Alyssa da karamin ministan ilimi Farfesa Suwaiba Said Ahmad bisa goyon baya da fahimtarsu.

 

COV ALIYU LAWAL.

 

Labarai

Labarai20 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara