Connect with us

Labarai

Katin Zabe: PDP Ta Bukaci Mambobinta Su Hanzarta Yin Rajista

Published

on

Jam’iyyar PDP reshen Jihar Kwara, ta bukaci magoya bayanta da ’yan jam’iyya a gida da waje su yi amfani da damar da Hukumar ZabjaMai Zaman Kantdata Kasa (INEC) ta bada na ci gaba da yin rajistar masu kada kuri’a (CVR) domin sabbin mambobi su yi rajista.

A cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na jam’iyyar a jihar, Olusegun Adewara, ya fitar, ya ce ya zama wajibi ga ’yan jam’iyyar PDP a fadin jihar, musamman manyan masu ruwa da tsaki, jami’an jam’iyya da masu neman takarar mukamai daban-daban, su dauki wannan rajista a matsayin babban aiki a mazabunsu.

Sanarwar ta bayyana cewa wannan rajista na daga cikin muhimman ginshikan fafutukar #RescueKwara (Ceto Jihar Kwara) da jam’iyyar ke yi domin zaben 2027.

Haka kuma sanarwar ta yi kira ga mambobin jam’iyyar da su bai wa wannan tsari fifiko, tare da mallakar katin zabe, wanda shi ne zai basu damar kada kuri’a a zabukan 2027.

Muna  tunatar da mambobinmu cewa katin zabe na dindindin (PVC) da INEC ke bayarwa shi ne kadai sahihin abu da masu kada kuri’a za su yi amfani da shi wajen gyara halin rashin tsaro, talauci da rashin shugabanci na gaskiya da ke damun jihar Kwara tun daga 2019,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta kuma bukaci mambobi, musamman masu ruwa da tsaki a jam’iyyar, jami’ai da masu neman mukaman siyasa daban-daban, da su tabbatar da bin wannan umarni a mazabunsu domin tabbatar da karfin jam’iyyar.

 

Ali Muhammad Rabi’u 

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara