Kasuwanci
Sanata Mai Wakiltar Kebbi Ta Tsakiya Ya Raba Kayayyakin Tallafi
Sanata mai wakiltar Kebbi ta tsakiya, Sanata Muhammad Adamu Aleiro, ya raba wa al’ummar mazabar sa kayan tallafi da nufin ba su damar dogaro da kai.
Kayayyakin sun hada da babura 150 (Keke NAPEP), babura 114, firiza mai zafin rana guda 302, injin nika 750, famfunan ruwa mai amfani da hasken rana 500, injin dinki 800 da kuma buhunan taki 3,400.
Da yake jawabi a wajen bikin raba kayayyakin a karamar hukumar Aleiro ta jihar Kebbi, Sanata Adamu Aleiro, ya ce hakan na daga cikin romon dimokuradiyya ga al’ummar mazabarsa kadai, har ma da jihar.
Sanata Aleiro, ya lissafo wasu ayyukan da ya aiwatar a matsayin aikin mazabu a kananan hukumomi takwas na mazabarsa da suka hada da hanyoyi, lafiya, ilimi, kawar da zaizayar kasa da kuma cibiyoyin koyon sana’o’i.
Ya shawarci gwamnan jihar Kebbi, Kwamared Nasiru Idris, da ya ci gaba da daukar muhimman ayyukan titunan gwamnatin tarayya a jihar, yana mai tabbatar da cewa a matsayinsu na ‘yan majalisa za su bi diddigin irin wadannan ayyuka domin ganin gwamnatin tarayya ta biya kudaden da aka kashe.
Shima da yake jawabi a wajen rabon kayayyakin, Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Nasiru Idris, ya yabawa Sanatan bisa yadda yake barbade al’ummarsa da ribar dimokuradiyya.
Gwamna Idris, ya bayar da tabbacin cewa gwamnatin sa ba ta taba hana wani dan majalisa damar samar da ayyukan mazabu ga jama’arsa ba yana mai cewa, duk wani aiki da za a kawo a Kebbi don amfanin al’ummar Kebbi ne.
Ya bukaci wadanda suka amfana da kada su sayar da kayayyakin, su yi amfani da su domin dogaro da kai.
COV/Abdullahi Tukur
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
