Connect with us

Labarai

Jami’an Tsaro Na Samun Nasara Akan Lakurawa a Jihar Kebbi

Published

on

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin Lakurawa ne da ba a tantance adadinsu ba, sun kai farmaki ga Alhaji Lawal Black Farm da wasu kauyukan Fulani da ke kusa da kauyen Natsini da ke karamar hukumar Argungu a jihar Kebbi, sun kashe ‘yan sanda biyu tare da sace wasu shanu da ba a tantance adadinsu ba.

 

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, SP Nafiu Abubakar, ya fitar, ya ce bayan samun rahoton, tawagar ‘yan sandan da ke sintiri ta garzaya zuwa wurin da lamarin ya faru, inda suka yi artabu da ‘yan bindigar, lamarin da ya tilasta wa ‘yan fashin tserewa, cikin dajin da raunukan harbin bindiga kuma an yi nasarar kwato wasu shanun da aka sace.

 

Sanarwar ta ce, kwamishinan ‘yan sanda Bello Mohammed Sani, ya kai ziyarar tantancewar a wurin, inda ya ziyarci mai martaba Sarkin Argungu, Alhaji Sama’ila Muhammad Mera, inda ya jajanta masa tare da yi masa bayani kan kokarin, na hadin gwiwar hukumomin tsaro wajen yaki da miyagun laifuka a yankin.

 

Yayin da yake jaddada kudirin rundunar na yaki da kalubalen tsaro a jihar Kebbi,

CP Sani, ya yi Allah wadai da wannan mummunan lamari, ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan jami’an ‘yan sandan da suka rasu ya kuma baiwa iyalansu da masu fatan alheri da juriyar wannan rashi mara misaltuwa.

 

PR/ Abdullahi Tukur/Wababe

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara