Connect with us

Fasaha

Majalisar Wakilai Za Ta Gayyaci Ministan Lafiya Ya Mata Bayani

Published

on

Majalisar wakilai za ta gayyaci ministan lafiya domin yiwa ‘yan Najeriya bayani kan yanayin da ya kai ga rashin aiwatar da ayyukan jinya kyauta ga mata masu juna biyu da da kuma bayan haihuwa.

Matakin dai ya biyo bayan kudirin da dan majalisa daga jihar Bauchi Alh Mohammed Dan Abba Shehu ya gabatar a zaman majalisar.

Da yake gabatar da kudirin, Alhaji Dan Abba Shehu, ya bayyana cewa gwamnati na ware kudade a cikin kasafin kudin shekara na cibiyoyin kula da lafiyar jama’a domin samar da ayyukan kiwon lafiya ga ‘yan kasa musamman mata masu juna biyu wadanda iyalansu ba sa iya samun magani

Dan majalisar wanda ya jaddada mahimmancin tsarin kiwon lafiya kyauta ga talakawan Najeriya, ya jaddada bukatar gwamnati ta ba da fifikon ayyukan da suka dace don baiwa mata masu juna biyu damar samun magani kyauta daga Cibiyar Kiwon Lafiyar Jama’a a lokacin haihuwa.

Ya bayyana damuwarsa cewa har yanzu Najeriya na fama da yawaitar cututtuka da ke haifar da mace-macen mata masu juna biyu a duk shekara.

Alhaji Dan Abba Shehu, ya jaddada cewa rashin kulawar gwamnati na bukatar cibiyoyin kiwon lafiyar jama’a su samu kwararrun likitocin su ba da kulawar da ta dace ga marasa lafiya ciki har da mata masu juna biyu a lokacin haihuwa domin magance matsalar.rikitarwa da kuma nemo mafita na dindindin ga barazanar.

Yayin da majalisar ta amince da kudirin, ta umarci kwamitinta na cibiyoyin kiwon lafiya da ya tabbatar da bin kudurorin.

COV: TSIBIRI/Wababe

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara