Fasaha
Majalisar Wakilai Za Ta Gayyaci Ministan Lafiya Ya Mata Bayani
Majalisar wakilai za ta gayyaci ministan lafiya domin yiwa ‘yan Najeriya bayani kan yanayin da ya kai ga rashin aiwatar da ayyukan jinya kyauta ga mata masu juna biyu da da kuma bayan haihuwa.
Matakin dai ya biyo bayan kudirin da dan majalisa daga jihar Bauchi Alh Mohammed Dan Abba Shehu ya gabatar a zaman majalisar.
Da yake gabatar da kudirin, Alhaji Dan Abba Shehu, ya bayyana cewa gwamnati na ware kudade a cikin kasafin kudin shekara na cibiyoyin kula da lafiyar jama’a domin samar da ayyukan kiwon lafiya ga ‘yan kasa musamman mata masu juna biyu wadanda iyalansu ba sa iya samun magani
Dan majalisar wanda ya jaddada mahimmancin tsarin kiwon lafiya kyauta ga talakawan Najeriya, ya jaddada bukatar gwamnati ta ba da fifikon ayyukan da suka dace don baiwa mata masu juna biyu damar samun magani kyauta daga Cibiyar Kiwon Lafiyar Jama’a a lokacin haihuwa.
Ya bayyana damuwarsa cewa har yanzu Najeriya na fama da yawaitar cututtuka da ke haifar da mace-macen mata masu juna biyu a duk shekara.
Alhaji Dan Abba Shehu, ya jaddada cewa rashin kulawar gwamnati na bukatar cibiyoyin kiwon lafiyar jama’a su samu kwararrun likitocin su ba da kulawar da ta dace ga marasa lafiya ciki har da mata masu juna biyu a lokacin haihuwa domin magance matsalar.rikitarwa da kuma nemo mafita na dindindin ga barazanar.
Yayin da majalisar ta amince da kudirin, ta umarci kwamitinta na cibiyoyin kiwon lafiya da ya tabbatar da bin kudurorin.
COV: TSIBIRI/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
