Connect with us

Labarai

Zamu Tabbatar Da Anyi Bukukuwan Sallah Lafiya A Kebbi – ‘CP Chris

Published

on

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kebbi, Chris Aimionowane, ya umurci, jami’an ‘yan sanda su ci gaba da aikin su na tabbatar da tsaro kafin da kuma lokaci da bayan bukukuwan Sallaha karama da za a fara gobe laraba..

 

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar ya fitar, ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar yayin da yake taya al’ummar musulmin jihar murnar kammala azumin watan Ramadan na bana yana yi wa daukacin al’ummar musulmi barka da Sallah.

 

Sanarwar ta yi kira ga al’ummar jihar da su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwan domin yin tunani da kuma yin addu’o’in zaman lafiya da ci gaban jihar da kasa baki daya.

 

Haka kuma ta yi kira ga malaman addini da masu ibada da mazauna jihar da su ba ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro hadin kai a jihar domin an samar da isasshen tsaro domin tabbatar da gudanar da bukukuwan sallah a jihar cikin kwanciyar hankali.

 

Yayin da yake gargadin duk masu tayar da hankali da mugun nufi da wani yunkurin kawo cikas ga bikin da su kaurace wa jihar, ya kuma umarci mutanen jihar Kebbi na gari da su ci gaba da zaman lafiya tare da gudanar da bukukuwa cikin kwanciyar hankali da lumana.

 

 

PR/Abdullahi Tukur/Wababe

Labarai

Labarai11 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara